فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ

Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).


فِي صُحُفٖ مُّكَرَّمَةٖ

(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,


مَّرۡفُوعَةٖ مُّطَهَّرَةِۭ

Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.


بِأَيۡدِي سَفَرَةٖ

A cikin hannãyen mala'iku marubũta.


كِرَامِۭ بَرَرَةٖ

Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.


قُتِلَ ٱلۡإِنسَٰنُ مَآ أَكۡفَرَهُۥ

An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!


مِنۡ أَيِّ شَيۡءٍ خَلَقَهُۥ

Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?


مِن نُّطۡفَةٍ خَلَقَهُۥ فَقَدَّرَهُۥ

Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).


ثُمَّ ٱلسَّبِيلَ يَسَّرَهُۥ

Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.


ثُمَّ أَمَاتَهُۥ فَأَقۡبَرَهُۥ

Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.


ثُمَّ إِذَا شَآءَ أَنشَرَهُۥ

Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.



الصفحة التالية
Icon