وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ كُشِطَتۡ

Kuma idan sama aka fẽɗe ta.


وَإِذَا ٱلۡجَحِيمُ سُعِّرَتۡ

Kuma idan Jahĩm aka hũra ta


وَإِذَا ٱلۡجَنَّةُ أُزۡلِفَتۡ

Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.


عَلِمَتۡ نَفۡسٞ مَّآ أَحۡضَرَتۡ

Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).


فَلَآ أُقۡسِمُ بِٱلۡخُنَّسِ

To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.


ٱلۡجَوَارِ ٱلۡكُنَّسِ

Mãsu gudu suna ɓũya.


وَٱلَّيۡلِ إِذَا عَسۡعَسَ

Da dare idan ya bãyar da bãya.


وَٱلصُّبۡحِ إِذَا تَنَفَّسَ

Da sãfiya idan ta yi lumfashi.


إِنَّهُۥ لَقَوۡلُ رَسُولٖ كَرِيمٖ

Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.


ذِي قُوَّةٍ عِندَ ذِي ٱلۡعَرۡشِ مَكِينٖ

Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.


مُّطَاعٖ ثَمَّ أَمِينٖ

Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.



الصفحة التالية
Icon