وَإِذَا قُرِئَ عَلَيۡهِمُ ٱلۡقُرۡءَانُ لَا يَسۡجُدُونَۤ۩

Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u?


بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ يُكَذِّبُونَ

Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.


وَٱللَّهُ أَعۡلَمُ بِمَا يُوعُونَ

Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.


فَبَشِّرۡهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٍ

Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.


إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ لَهُمۡ أَجۡرٌ غَيۡرُ مَمۡنُونِۭ

Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa.



الصفحة التالية
Icon