إِذِ ٱنۢبَعَثَ أَشۡقَىٰهَا

A lõkacin da mafi shaƙãwarsu ya tafi (wurin sõke rãkumar sãlihu).


فَقَالَ لَهُمۡ رَسُولُ ٱللَّهِ نَاقَةَ ٱللَّهِ وَسُقۡيَٰهَا

Sai Manzon Allah ya gaya musu cewa: "Ina tsõratar da ku ga rãƙumar Allah da ruwan shanta!"


فَكَذَّبُوهُ فَعَقَرُوهَا فَدَمۡدَمَ عَلَيۡهِمۡ رَبُّهُم بِذَنۢبِهِمۡ فَسَوَّىٰهَا

Sai suka ƙaryata shi, sa'an nan suka sõke ta. Sabõda haka Ubangijinsu Ya darkãke su, sabõda zunubinsu. Sa'an nan Ya daidaita ta (azãbar ga mai laifi da maras laifi).


وَلَا يَخَافُ عُقۡبَٰهَا

Kuma bã ya tsõron ãƙibarta (ita halakãwar).



الصفحة التالية
Icon