فَلَا تَعۡجَلۡ عَلَيۡهِمۡۖ إِنَّمَا نَعُدُّ لَهُمۡ عَدّٗا

Sabõda haka kada ka yi gaggawa a kansu, Munã yi musu ƙidãyar ajali ne kawai, ƙidãyãwa.


يَوۡمَ نَحۡشُرُ ٱلۡمُتَّقِينَ إِلَى ٱلرَّحۡمَٰنِ وَفۡدٗا

A rãnar da Muka tãra mãsu taƙawa zuwa ga Mai rahama sunã bãƙin girma.


وَنَسُوقُ ٱلۡمُجۡرِمِينَ إِلَىٰ جَهَنَّمَ وِرۡدٗا

Kuma Munã kõra mãsu laifi zuwa Jahannama, gargaãwa.


لَّا يَمۡلِكُونَ ٱلشَّفَٰعَةَ إِلَّا مَنِ ٱتَّخَذَ عِندَ ٱلرَّحۡمَٰنِ عَهۡدٗا

Ba su mal1akar cẽto fãce wanda ya riƙi alkawari a wurin Mai rahama.


وَقَالُواْ ٱتَّخَذَ ٱلرَّحۡمَٰنُ وَلَدٗا

Kuma suka ce: "Mai rahama Yã riƙi ã!"


لَّقَدۡ جِئۡتُمۡ شَيۡـًٔا إِدّٗا

Lalle ne haƙĩƙa kun zo da wani abu mai girman mũni.


تَكَادُ ٱلسَّمَٰوَٰتُ يَتَفَطَّرۡنَ مِنۡهُ وَتَنشَقُّ ٱلۡأَرۡضُ وَتَخِرُّ ٱلۡجِبَالُ هَدًّا

Sammai sunã kusa su tsattsage sabõda shi, kuma ƙasa ke kẽce kuma duwãtsu su faɗi sunã karyayyu.


أَن دَعَوۡاْ لِلرَّحۡمَٰنِ وَلَدٗا

Dõmin sun yi da'awar ɗã ga Mai rahama.



الصفحة التالية
Icon