إِنَّهُمۡ أَلۡفَوۡاْ ءَابَآءَهُمۡ ضَآلِّينَ

Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.


فَهُمۡ عَلَىٰٓ ءَاثَٰرِهِمۡ يُهۡرَعُونَ

Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.


وَلَقَدۡ ضَلَّ قَبۡلَهُمۡ أَكۡثَرُ ٱلۡأَوَّلِينَ

Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.


وَلَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا فِيهِم مُّنذِرِينَ

Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.


فَٱنظُرۡ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلۡمُنذَرِينَ

Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.


إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلۡمُخۡلَصِينَ

Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.


وَلَقَدۡ نَادَىٰنَا نُوحٞ فَلَنِعۡمَ ٱلۡمُجِيبُونَ

Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.


وَنَجَّيۡنَٰهُ وَأَهۡلَهُۥ مِنَ ٱلۡكَرۡبِ ٱلۡعَظِيمِ

Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.


وَجَعَلۡنَا ذُرِّيَّتَهُۥ هُمُ ٱلۡبَاقِينَ

Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.



الصفحة التالية
Icon