فَمَا ظَنُّكُم بِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

"To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"


فَنَظَرَ نَظۡرَةٗ فِي ٱلنُّجُومِ

Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.


فَقَالَ إِنِّي سَقِيمٞ

Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."


فَتَوَلَّوۡاْ عَنۡهُ مُدۡبِرِينَ

Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.


فَرَاغَ إِلَىٰٓ ءَالِهَتِهِمۡ فَقَالَ أَلَا تَأۡكُلُونَ

Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?


مَا لَكُمۡ لَا تَنطِقُونَ

"Me ya sãme ku, bã ku magana?"


فَرَاغَ عَلَيۡهِمۡ ضَرۡبَۢا بِٱلۡيَمِينِ

Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.


فَأَقۡبَلُوٓاْ إِلَيۡهِ يَزِفُّونَ

Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.


قَالَ أَتَعۡبُدُونَ مَا تَنۡحِتُونَ

Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,


وَٱللَّهُ خَلَقَكُمۡ وَمَا تَعۡمَلُونَ

"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"



الصفحة التالية
Icon