فَأۡتُواْ بِكِتَٰبِكُمۡ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.


وَجَعَلُواْ بَيۡنَهُۥ وَبَيۡنَ ٱلۡجِنَّةِ نَسَبٗاۚ وَلَقَدۡ عَلِمَتِ ٱلۡجِنَّةُ إِنَّهُمۡ لَمُحۡضَرُونَ

Kuma suka sanya nasaba a tsakãninSa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"


سُبۡحَٰنَ ٱللَّهِ عَمَّا يَصِفُونَ

Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.


إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلۡمُخۡلَصِينَ

Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.


فَإِنَّكُمۡ وَمَا تَعۡبُدُونَ

To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,


مَآ أَنتُمۡ عَلَيۡهِ بِفَٰتِنِينَ

Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi.


إِلَّا مَنۡ هُوَ صَالِ ٱلۡجَحِيمِ

Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.


وَمَامِنَّآ إِلَّا لَهُۥ مَقَامٞ مَّعۡلُومٞ

"Kuma bãbu kõwa daga cikinmu, fãce yanã da matsayi sananne."


وَإِنَّا لَنَحۡنُ ٱلصَّآفُّونَ

"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."



الصفحة التالية
Icon