Sai wanda Ubangijinka Ya yi wa rahama, kuma dõmin wannan* ne Ya halicce su. Kuma kalmar "Ubangijinka" Lalle ne zã Ni cika Jahannama da aljannu da mutãne gaba ɗaya" ta cika.
____________________
* Allah ya halicci mutãne da hãlãye dabam-dabam dõmin su sãɓa wa jũna.