Kuma a gittã* su ga Ubangijinka sunã sahu guda, (Mu ce musu), "Lalle ne haƙĩƙa kun zo Mana, kamar yadda Muka halitta ku a farkon lõkaci. Ã'a, kun riya cẽwa bã zã Mu sanya mukuwani lõkacin haɗuwa ba."
____________________
 * Bayãnin abũbuwan da ke aukuwa a wurin hisãbi ke nan ga mãsu bin son zũciya, su bar sharĩ'a.


الصفحة التالية
Icon