Gõdiya ta tabbata ga Allah wanda Ya halitta sammai da ƙasa, kuma Ya sanya duffai da haske*, sa'an nan kuma waɗanda suka kãfirta, da Ubangijinsu suke karkacewa.
____________________
* Duffai na dare da zãlunci da bin hukunce-hukuncen al'ãdu, haske kuma shĩ ne na taurãri da wuta da shari'u na Littãfi da annabci.


الصفحة التالية
Icon