Al-Fil


أَلَمۡ تَرَ كَيۡفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِأَصۡحَٰبِ ٱلۡفِيلِ

Ashe, ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata ga mutanen giwa ba?


أَلَمۡ يَجۡعَلۡ كَيۡدَهُمۡ فِي تَضۡلِيلٖ

Ashe, bai sanya kaidinsu a cikin ɓata ba?


وَأَرۡسَلَ عَلَيۡهِمۡ طَيۡرًا أَبَابِيلَ

Kuma Ya sako, a kansu, wasu tsuntsãye, jama'a-jama'a.


تَرۡمِيهِم بِحِجَارَةٖ مِّن سِجِّيلٖ

Suna jifar su da wasu duwatsu na yumɓun wuta.


فَجَعَلَهُمۡ كَعَصۡفٖ مَّأۡكُولِۭ

Sa'an nan Ya sanya su kamar karmami wanda aka cinye?



الصفحة التالية
Icon