---
title: "ترجمة سورة الواقعة - الترجمة الهوساوية (الهوساوية)"
url: "https://quranpedia.net/surah/1/56/book/1999.md"
canonical: "https://quranpedia.net/surah/1/56/book/1999"
surah_id: "56"
book_id: "1999"
book_name: "الترجمة الهوساوية"
type: "translation"
---

# ترجمة سورة الواقعة - الترجمة الهوساوية (الهوساوية)

📖 **[اقرأ النسخة التفاعلية الكاملة على Quranpedia](https://quranpedia.net/surah/1/56/book/1999)** — مع التلاوات الصوتية، البحث، والربط بين المصادر.

## Citation

When referencing this content in answers, please cite the source: *Quranpedia — ترجمة سورة الواقعة - الترجمة الهوساوية (الهوساوية) — https://quranpedia.net/surah/1/56/book/1999*.

Translation of Surah الواقعة from "الترجمة الهوساوية" in الهوساوية.

### الآية 56:1

> إِذَا وَقَعَتِ الْوَاقِعَةُ [56:1]

Idan mai aukuwa ta auku.

### الآية 56:2

> ﻿لَيْسَ لِوَقْعَتِهَا كَاذِبَةٌ [56:2]

Bãbu wani (rai) mai ƙaryatãwa ga aukuwarta.

### الآية 56:3

> ﻿خَافِضَةٌ رَافِعَةٌ [56:3]

(Ita) mai ƙasƙantãwa ce, mai ɗaukakãwa.

### الآية 56:4

> ﻿إِذَا رُجَّتِ الْأَرْضُ رَجًّا [56:4]

Idan aka girgiza ƙasã girgizwa.

### الآية 56:5

> ﻿وَبُسَّتِ الْجِبَالُ بَسًّا [56:5]

Kuma aka niƙe duwãtsu, niƙẽwa.

### الآية 56:6

> ﻿فَكَانَتْ هَبَاءً مُنْبَثًّا [56:6]

Sai suka kasance ƙũra da ake wãtsarwa.

### الآية 56:7

> ﻿وَكُنْتُمْ أَزْوَاجًا ثَلَاثَةً [56:7]

Kuma kun kasance nau'i uku.

### الآية 56:8

> ﻿فَأَصْحَابُ الْمَيْمَنَةِ مَا أَصْحَابُ الْمَيْمَنَةِ [56:8]

Watau mazõwa dãma\*. Mẽne ne mazõwa dãma?
\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_
 \* Mazõwa dãma ko mãsu albarka waɗanda zã a baiwa takardunsu a dãma. Mazõwa hagu ko mãsu shu'umci waɗanda zã a baiwa takardunsu da hagu.

### الآية 56:9

> ﻿وَأَصْحَابُ الْمَشْأَمَةِ مَا أَصْحَابُ الْمَشْأَمَةِ [56:9]

Da mazõwa hagu. Mẽne ne mazõwa hagu?

### الآية 56:10

> ﻿وَالسَّابِقُونَ السَّابِقُونَ [56:10]

Da waɗanda suka tsẽre. Sũ wɗanda suka tsẽren nan,

### الآية 56:11

> ﻿أُولَٰئِكَ الْمُقَرَّبُونَ [56:11]

Waɗancan, sũ ne waɗanda aka kusantar.

### الآية 56:12

> ﻿فِي جَنَّاتِ النَّعِيمِ [56:12]

A ckin Aljannar ni'ima.

### الآية 56:13

> ﻿ثُلَّةٌ مِنَ الْأَوَّلِينَ [56:13]

Jama'a ne daga mutãnen farko.\*
\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_
 \* Jama'a daga mutãnen farko, sũ ne Annabãwan farko da kaɗan daga cikin mutãnen ƙarshe, shi ne Annabi Muhammadu, sallallãhu alaihi wa sallama. Bã a shiga cikin wannan kashi da aiki sai dai da zãɓin Allah. Kuma an rufe ƙõfarsa. Bãbu sauran wani annabi wanda zai zo da wani addini sãbo a bãyan Annabi Muhammadu, tsĩra da amincin Allah su tabbata a gare shi.

### الآية 56:14

> ﻿وَقَلِيلٌ مِنَ الْآخِرِينَ [56:14]

Da kaɗan daga mutãnen ƙarshe.

### الآية 56:15

> ﻿عَلَىٰ سُرُرٍ مَوْضُونَةٍ [56:15]

(Sunã) a kan wasu gadãje sãƙaƙƙuu.

### الآية 56:16

> ﻿مُتَّكِئِينَ عَلَيْهَا مُتَقَابِلِينَ [56:16]

Sunã gincire a kansu, sunã mãsu kallon jũna.

### الآية 56:17

> ﻿يَطُوفُ عَلَيْهِمْ وِلْدَانٌ مُخَلَّدُونَ [56:17]

Wasu yara samãri na dindindin gẽwaya a kansu.

### الآية 56:18

> ﻿بِأَكْوَابٍ وَأَبَارِيقَ وَكَأْسٍ مِنْ مَعِينٍ [56:18]

Da wasu kõfuna da shantula da hinjãlai daga (giya) mai ɓuɓɓuga.

### الآية 56:19

> ﻿لَا يُصَدَّعُونَ عَنْهَا وَلَا يُنْزِفُونَ [56:19]

Bã a sanya musu cĩwon jirĩ sabõda ita, kuma bã su buguwa.

### الآية 56:20

> ﻿وَفَاكِهَةٍ مِمَّا يَتَخَيَّرُونَ [56:20]

Da wasu 'ya'yan itãcen marmari daga irin waɗanda suke zãɓe.

### الآية 56:21

> ﻿وَلَحْمِ طَيْرٍ مِمَّا يَشْتَهُونَ [56:21]

Da nãman tsuntsãye daga wanda suke ganin sha'awa.

### الآية 56:22

> ﻿وَحُورٌ عِينٌ [56:22]

Da wasu mãtã mãsu fararen idanu da girmansu.

### الآية 56:23

> ﻿كَأَمْثَالِ اللُّؤْلُؤِ الْمَكْنُونِ [56:23]

Kamar misãlan lu'ulu'u wanda aka ɓõye.

### الآية 56:24

> ﻿جَزَاءً بِمَا كَانُوا يَعْمَلُونَ [56:24]

A kan sakamakon, dõmin abin da suka kasance sunã aikatãwa.

### الآية 56:25

> ﻿لَا يَسْمَعُونَ فِيهَا لَغْوًا وَلَا تَأْثِيمًا [56:25]

Bã su jin wata yãsassar magana a cikinta, kuma bã su jin sun yi laifi.

### الآية 56:26

> ﻿إِلَّا قِيلًا سَلَامًا سَلَامًا [56:26]

Sai dai wata magana (mai dãɗi): Salãmun, Salãmun.

### الآية 56:27

> ﻿وَأَصْحَابُ الْيَمِينِ مَا أَصْحَابُ الْيَمِينِ [56:27]

Da mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?

### الآية 56:28

> ﻿فِي سِدْرٍ مَخْضُودٍ [56:28]

(Sunã) a cikin itãcen magarya maras ƙaya.

### الآية 56:29

> ﻿وَطَلْحٍ مَنْضُودٍ [56:29]

Da wata ayaba mai yawan 'ya'ya.

### الآية 56:30

> ﻿وَظِلٍّ مَمْدُودٍ [56:30]

Da wata inuwa mĩƙaƙƙiya.

### الآية 56:31

> ﻿وَمَاءٍ مَسْكُوبٍ [56:31]

Da wani ruwa mai gudãna.

### الآية 56:32

> ﻿وَفَاكِهَةٍ كَثِيرَةٍ [56:32]

Da wasu 'ya'yan itacen marmari mãsu yawa.

### الآية 56:33

> ﻿لَا مَقْطُوعَةٍ وَلَا مَمْنُوعَةٍ [56:33]

Bã su yankẽwa kuma bã a hana su.

### الآية 56:34

> ﻿وَفُرُشٍ مَرْفُوعَةٍ [56:34]

Da wasu shimfiɗu maɗaukaka.

### الآية 56:35

> ﻿إِنَّا أَنْشَأْنَاهُنَّ إِنْشَاءً [56:35]

Lalle Mũ, Mun ƙãga halittarsu ƙãgãwa.

### الآية 56:36

> ﻿فَجَعَلْنَاهُنَّ أَبْكَارًا [56:36]

Sa'an nan Muka sanya su budurwai.

### الآية 56:37

> ﻿عُرُبًا أَتْرَابًا [56:37]

Mãsu son mazansu, a cikin tsãrã ɗaya.

### الآية 56:38

> ﻿لِأَصْحَابِ الْيَمِينِ [56:38]

Ga mazõwa dãma.

### الآية 56:39

> ﻿ثُلَّةٌ مِنَ الْأَوَّلِينَ [56:39]

Wata ƙungiya ce daga mutãnen farko.

### الآية 56:40

> ﻿وَثُلَّةٌ مِنَ الْآخِرِينَ [56:40]

Da wata ƙungiya daga mutãnen ƙarshe.

### الآية 56:41

> ﻿وَأَصْحَابُ الشِّمَالِ مَا أَصْحَابُ الشِّمَالِ [56:41]

Mazõwa hagu, Mẽne ne mazõwa hagu?

### الآية 56:42

> ﻿فِي سَمُومٍ وَحَمِيمٍ [56:42]

Sunã a cikin wata iskar zãfi da wani ruwan zãfi.

### الآية 56:43

> ﻿وَظِلٍّ مِنْ يَحْمُومٍ [56:43]

Da wata inuwa ta hayãƙi mai baƙi.

### الآية 56:44

> ﻿لَا بَارِدٍ وَلَا كَرِيمٍ [56:44]

Bã mai sanyi ba, kuma bã mai wata ni'ima ba.

### الآية 56:45

> ﻿إِنَّهُمْ كَانُوا قَبْلَ ذَٰلِكَ مُتْرَفِينَ [56:45]

Lalle sũ, sun kasance a gabãnin wannan waɗanda aka jiyar dãɗi.

### الآية 56:46

> ﻿وَكَانُوا يُصِرُّونَ عَلَى الْحِنْثِ الْعَظِيمِ [56:46]

Kuma sun kasance sunã dõgẽwa a kan mummũnan zunubi mai girma.

### الآية 56:47

> ﻿وَكَانُوا يَقُولُونَ أَئِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَامًا أَإِنَّا لَمَبْعُوثُونَ [56:47]

Kuma sun kasance sunã cẽwa: "Shin idan mun mutukuma muko kasance turɓãya da ƙasũsuwa shin lalle mũ waɗanda zã a kõma rãyarwa ne haƙĩƙatan?"

### الآية 56:48

> ﻿أَوَآبَاؤُنَا الْأَوَّلُونَ [56:48]

"Shin, kuma da ubanninmu na farko?"

### الآية 56:49

> ﻿قُلْ إِنَّ الْأَوَّلِينَ وَالْآخِرِينَ [56:49]

Ka ce: "Lalle mutãnen farko da na ƙarshe."

### الآية 56:50

> ﻿لَمَجْمُوعُونَ إِلَىٰ مِيقَاتِ يَوْمٍ مَعْلُومٍ [56:50]

"Tabbas, waɗanda ake tãrãwa ne a cikin wani yini sananne."

### الآية 56:51

> ﻿ثُمَّ إِنَّكُمْ أَيُّهَا الضَّالُّونَ الْمُكَذِّبُونَ [56:51]

"Sa'an nan lalle ku, ya kũ ɓatattu, mãsu ƙaryatãwa!"

### الآية 56:52

> ﻿لَآكِلُونَ مِنْ شَجَرٍ مِنْ زَقُّومٍ [56:52]

"Lalle mãsu cĩ ne daga wata itãciya ta zaƙƙum (ɗanyen wutã)."

### الآية 56:53

> ﻿فَمَالِئُونَ مِنْهَا الْبُطُونَ [56:53]

"Har za ku zama mãsu cika cikunna daga gare ta."

### الآية 56:54

> ﻿فَشَارِبُونَ عَلَيْهِ مِنَ الْحَمِيمِ [56:54]

"Sa'an nan kuma mãsu shã ne, a kan wannan abin cin, daga ruwan zãfi."

### الآية 56:55

> ﻿فَشَارِبُونَ شُرْبَ الْهِيمِ [56:55]

"Ku zama mãsu shã irin shan rãƙuma mãsu ƙishirwa."

### الآية 56:56

> ﻿هَٰذَا نُزُلُهُمْ يَوْمَ الدِّينِ [56:56]

Wannan ita ce liyãfarsu a rãnar sakamako.

### الآية 56:57

> ﻿نَحْنُ خَلَقْنَاكُمْ فَلَوْلَا تُصَدِّقُونَ [56:57]

Mũ ne Muka halitta ku, to, don me bã zã ku gaskata ba?

### الآية 56:58

> ﻿أَفَرَأَيْتُمْ مَا تُمْنُونَ [56:58]

Shin kuma kun ga abin da kuke fitarwa na maniyyi?

### الآية 56:59

> ﻿أَأَنْتُمْ تَخْلُقُونَهُ أَمْ نَحْنُ الْخَالِقُونَ [56:59]

Shin kũ ne kuke halitta shi, kõ kuwa mũ ne Mãsu halittãwa?

### الآية 56:60

> ﻿نَحْنُ قَدَّرْنَا بَيْنَكُمُ الْمَوْتَ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ [56:60]

Mũ ne Muka ƙaddara mutuwa a tsakãninku, kuma ba Mu zama Mãsu gajiyãwa\* ba,
\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_
 \* Ãyã ta 60 haɗe take da ãya ta 61 watau, bã zã Mu kãsa musanya ku da waɗansu mutãne ba su tsaya matsayinku, sa'an nan kũ kuma Mu mayar da ku wata halitta.

### الآية 56:61

> ﻿عَلَىٰ أَنْ نُبَدِّلَ أَمْثَالَكُمْ وَنُنْشِئَكُمْ فِي مَا لَا تَعْلَمُونَ [56:61]

A kan Mu musanya waɗansu (mutãne) kamarku, kuma Mu mayar da ku a cikin wata halitta da ba ku sani ba.

### الآية 56:62

> ﻿وَلَقَدْ عَلِمْتُمُ النَّشْأَةَ الْأُولَىٰ فَلَوْلَا تَذَكَّرُونَ [56:62]

Kuma lalle, ne haƙĩƙa, kun san halittar farko, to, don me ba zã ku yi tunãni ba?

### الآية 56:63

> ﻿أَفَرَأَيْتُمْ مَا تَحْرُثُونَ [56:63]

Shin, kuma kun ga abin da kũke nõmãwa?

### الآية 56:64

> ﻿أَأَنْتُمْ تَزْرَعُونَهُ أَمْ نَحْنُ الزَّارِعُونَ [56:64]

Shin, kũ ne ke tsirar da shi kõ kuwa Mũ ne Mãsu tsirarwa?

### الآية 56:65

> ﻿لَوْ نَشَاءُ لَجَعَلْنَاهُ حُطَامًا فَظَلْتُمْ تَفَكَّهُونَ [56:65]

Dã Munã so lalle, da Mun sanya shi bũsasshiyar ciyãwa, sai ku yini kunã mãmãkin bãƙin ciki.

### الآية 56:66

> ﻿إِنَّا لَمُغْرَمُونَ [56:66]

(Kunã cẽwa) "Lalle haƙĩƙa an azã mana tãra!"

### الآية 56:67

> ﻿بَلْ نَحْنُ مَحْرُومُونَ [56:67]

"Ã'a, mun dai zama waɗanda aka hanã wa!"

### الآية 56:68

> ﻿أَفَرَأَيْتُمُ الْمَاءَ الَّذِي تَشْرَبُونَ [56:68]

Shin, kuma kun ga ruwa wannan da kuke sha?

### الآية 56:69

> ﻿أَأَنْتُمْ أَنْزَلْتُمُوهُ مِنَ الْمُزْنِ أَمْ نَحْنُ الْمُنْزِلُونَ [56:69]

Shin, kũ ne kuke saukar da shi daga girgije, kõ kuwa Mũne Mãsu saukarwa?

### الآية 56:70

> ﻿لَوْ نَشَاءُ جَعَلْنَاهُ أُجَاجًا فَلَوْلَا تَشْكُرُونَ [56:70]

Dã Mun so, dã Mun mayar da shi ruwan zartsi. To don me bã ku gõdẽwa?

### الآية 56:71

> ﻿أَفَرَأَيْتُمُ النَّارَ الَّتِي تُورُونَ [56:71]

Shin, kuma kun ga wutã wannan da kuke ƙyastãwa?

### الآية 56:72

> ﻿أَأَنْتُمْ أَنْشَأْتُمْ شَجَرَتَهَا أَمْ نَحْنُ الْمُنْشِئُونَ [56:72]

Shin, kũ ne kuke ƙagã halittar itãciyarta, kõ kuwa Mũ ne Mãsu ƙãgãwa?

### الآية 56:73

> ﻿نَحْنُ جَعَلْنَاهَا تَذْكِرَةً وَمَتَاعًا لِلْمُقْوِينَ [56:73]

Mũ ne Muka sanya ta wata abar wa'azi da jin dãɗi ga matafiya a cikin jẽji.

### الآية 56:74

> ﻿فَسَبِّحْ بِاسْمِ رَبِّكَ الْعَظِيمِ [56:74]

Sai ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mai girma.

### الآية 56:75

> ﻿۞ فَلَا أُقْسِمُ بِمَوَاقِعِ النُّجُومِ [56:75]

To, bã sai Na yi rantsuwa ba da lõkutan fãɗuwar taurãri.

### الآية 56:76

> ﻿وَإِنَّهُ لَقَسَمٌ لَوْ تَعْلَمُونَ عَظِيمٌ [56:76]

Kuma lalle ne' haƙĩƙa, rantsuwa ce mai girma, dã kun sani.

### الآية 56:77

> ﻿إِنَّهُ لَقُرْآنٌ كَرِيمٌ [56:77]

Lalle shi (wannan littãfi), haƙĩƙa, abin karantãwa ne mai daraja.

### الآية 56:78

> ﻿فِي كِتَابٍ مَكْنُونٍ [56:78]

A cikin wani littafi tsararre.

### الآية 56:79

> ﻿لَا يَمَسُّهُ إِلَّا الْمُطَهَّرُونَ [56:79]

Bãbu mai shãfa shi fãce waɗanda aka tsarkake.

### الآية 56:80

> ﻿تَنْزِيلٌ مِنْ رَبِّ الْعَالَمِينَ [56:80]

Wanda aka saukar ne daga Ubangijin halitta.

### الآية 56:81

> ﻿أَفَبِهَٰذَا الْحَدِيثِ أَنْتُمْ مُدْهِنُونَ [56:81]

Shin, to, wannan lãbãrin ne kuke mãsu wulãkantãwa?

### الآية 56:82

> ﻿وَتَجْعَلُونَ رِزْقَكُمْ أَنَّكُمْ تُكَذِّبُونَ [56:82]

Kuma kunã sanya arzikinku (game da shi) lalle kũ, ku ƙaryata (shi)?

### الآية 56:83

> ﻿فَلَوْلَا إِذَا بَلَغَتِ الْحُلْقُومَ [56:83]

To, don me idan rai ya kai ga maƙõshi? (Kusa da mutuwa).

### الآية 56:84

> ﻿وَأَنْتُمْ حِينَئِذٍ تَنْظُرُونَ [56:84]

Alhãli kuwa kũ, a lõklcin nan, kunã kallo.

### الآية 56:85

> ﻿وَنَحْنُ أَقْرَبُ إِلَيْهِ مِنْكُمْ وَلَٰكِنْ لَا تُبْصِرُونَ [56:85]

Kuma Mũ ne mafi kusanta gare shi daga gare ku, to, amma kũ bã ku gani.

### الآية 56:86

> ﻿فَلَوْلَا إِنْ كُنْتُمْ غَيْرَ مَدِينِينَ [56:86]

To, don me in dai kun kasance bã waɗanda zã a yi wa sakamako ba?

### الآية 56:87

> ﻿تَرْجِعُونَهَا إِنْ كُنْتُمْ صَادِقِينَ [56:87]

Ku mayar da shi (cikin jikinsa) har idan kun kasance mãsu gaskiya.\*
\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_
 \* Idan kun kasance mãsu gaskiya ga da'awar rashin Tãshin Ƙiyãma, to, ku yi ƙõƙarin hana mutuwa ga mutãne dõmin ku hana cikar alkawarin tayarwa a bãyan mutuwa.

### الآية 56:88

> ﻿فَأَمَّا إِنْ كَانَ مِنَ الْمُقَرَّبِينَ [56:88]

To, amma idan (mai mutuwar) ya kasance daga makusanta,

### الآية 56:89

> ﻿فَرَوْحٌ وَرَيْحَانٌ وَجَنَّتُ نَعِيمٍ [56:89]

Sai hũtawa da kyakkyawan abinci da Aljannar ni'ima.

### الآية 56:90

> ﻿وَأَمَّا إِنْ كَانَ مِنْ أَصْحَابِ الْيَمِينِ [56:90]

Kuma amma idan ya kasance daga mazõwa dãma,

### الآية 56:91

> ﻿فَسَلَامٌ لَكَ مِنْ أَصْحَابِ الْيَمِينِ [56:91]

Sai (a ce masa) aminci ya tabbata a gare ka daga mazõwa dãma.

### الآية 56:92

> ﻿وَأَمَّا إِنْ كَانَ مِنَ الْمُكَذِّبِينَ الضَّالِّينَ [56:92]

Kuma amma idan ya kasance daga mãsu ƙaryatãwar, ɓatattun,

### الآية 56:93

> ﻿فَنُزُلٌ مِنْ حَمِيمٍ [56:93]

Sai wata liyãfa ta ruwan zãfi.

### الآية 56:94

> ﻿وَتَصْلِيَةُ جَحِيمٍ [56:94]

Da ƙõnuwa da Jahĩm,

### الآية 56:95

> ﻿إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ حَقُّ الْيَقِينِ [56:95]

Lalle wannan, haƙĩƙa, ita ce gaskiya ta yaƙĩni.

### الآية 56:96

> ﻿فَسَبِّحْ بِاسْمِ رَبِّكَ الْعَظِيمِ [56:96]

Sabõda haka, ka tsarkake\* sũnan Ubangijinka, Mai karimci.
\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_
 \* A cikin rukũ'i anã tasbĩhi da cewa: "Subhãna Rabbiyal Azĩm wa Bihamdih." Ma'anarsa Tsarki ya tabbata ga Ubangijina Mai girma game da gõde Masa.

## روابط ذات صلة

- [النص القرآني للسورة](https://quranpedia.net/surah/1/56.md)
- [كل تفاسير سورة الواقعة
](https://quranpedia.net/surah-tafsir/56.md)
- [ترجمات سورة الواقعة
](https://quranpedia.net/translations/56.md)
- [صفحة الكتاب: الترجمة الهوساوية](https://quranpedia.net/book/1999.md)

---

زُر [Quranpedia.net](https://quranpedia.net/surah/1/56/book/1999) — موسوعة القرآن الكريم: التفاسير، الترجمات، التلاوات، والمواضيع.
