---
title: "ترجمة سورة النازعات - الترجمة الهوساوية (الهوساوية)"
url: "https://quranpedia.net/surah/1/79/book/1999.md"
canonical: "https://quranpedia.net/surah/1/79/book/1999"
surah_id: "79"
book_id: "1999"
book_name: "الترجمة الهوساوية"
type: "translation"
---

# ترجمة سورة النازعات - الترجمة الهوساوية (الهوساوية)

📖 **[اقرأ النسخة التفاعلية الكاملة على Quranpedia](https://quranpedia.net/surah/1/79/book/1999)** — مع التلاوات الصوتية، البحث، والربط بين المصادر.

## Citation

When referencing this content in answers, please cite the source: *Quranpedia — ترجمة سورة النازعات - الترجمة الهوساوية (الهوساوية) — https://quranpedia.net/surah/1/79/book/1999*.

Translation of Surah النازعات from "الترجمة الهوساوية" in الهوساوية.

### الآية 79:1

> وَالنَّازِعَاتِ غَرْقًا [79:1]

Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.

### الآية 79:2

> ﻿وَالنَّاشِطَاتِ نَشْطًا [79:2]

Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.

### الآية 79:3

> ﻿وَالسَّابِحَاتِ سَبْحًا [79:3]

Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.

### الآية 79:4

> ﻿فَالسَّابِقَاتِ سَبْقًا [79:4]

Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.

### الآية 79:5

> ﻿فَالْمُدَبِّرَاتِ أَمْرًا [79:5]

Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.

### الآية 79:6

> ﻿يَوْمَ تَرْجُفُ الرَّاجِفَةُ [79:6]

Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.

### الآية 79:7

> ﻿تَتْبَعُهَا الرَّادِفَةُ [79:7]

Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.

### الآية 79:8

> ﻿قُلُوبٌ يَوْمَئِذٍ وَاجِفَةٌ [79:8]

Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.

### الآية 79:9

> ﻿أَبْصَارُهَا خَاشِعَةٌ [79:9]

Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.

### الآية 79:10

> ﻿يَقُولُونَ أَإِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِي الْحَافِرَةِ [79:10]

Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?

### الآية 79:11

> ﻿أَإِذَا كُنَّا عِظَامًا نَخِرَةً [79:11]

"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"

### الآية 79:12

> ﻿قَالُوا تِلْكَ إِذًا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌ [79:12]

Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"

### الآية 79:13

> ﻿فَإِنَّمَا هِيَ زَجْرَةٌ وَاحِدَةٌ [79:13]

To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.

### الآية 79:14

> ﻿فَإِذَا هُمْ بِالسَّاهِرَةِ [79:14]

Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.

### الآية 79:15

> ﻿هَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ مُوسَىٰ [79:15]

Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?

### الآية 79:16

> ﻿إِذْ نَادَاهُ رَبُّهُ بِالْوَادِ الْمُقَدَّسِ طُوًى [79:16]

A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?

### الآية 79:17

> ﻿اذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُ طَغَىٰ [79:17]

Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.

### الآية 79:18

> ﻿فَقُلْ هَلْ لَكَ إِلَىٰ أَنْ تَزَكَّىٰ [79:18]

"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.

### الآية 79:19

> ﻿وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ [79:19]

"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"

### الآية 79:20

> ﻿فَأَرَاهُ الْآيَةَ الْكُبْرَىٰ [79:20]

Sai ya nũna masa ãyar\* nan mafi girma.
\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_\_
 \* Ãyar Mũsã da ta fi girma ita ce sandarsa mai zama maciji ko hannunsa mai haske kamar tõcila idan yã sanya cikin hammata yã fitar.

### الآية 79:21

> ﻿فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ [79:21]

Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),

### الآية 79:22

> ﻿ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ [79:22]

Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.

### الآية 79:23

> ﻿فَحَشَرَ فَنَادَىٰ [79:23]

Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.

### الآية 79:24

> ﻿فَقَالَ أَنَا رَبُّكُمُ الْأَعْلَىٰ [79:24]

Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."

### الآية 79:25

> ﻿فَأَخَذَهُ اللَّهُ نَكَالَ الْآخِرَةِ وَالْأُولَىٰ [79:25]

Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.

### الآية 79:26

> ﻿إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَعِبْرَةً لِمَنْ يَخْشَىٰ [79:26]

Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.

### الآية 79:27

> ﻿أَأَنْتُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَمِ السَّمَاءُ ۚ بَنَاهَا [79:27]

Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.

### الآية 79:28

> ﻿رَفَعَ سَمْكَهَا فَسَوَّاهَا [79:28]

Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.

### الآية 79:29

> ﻿وَأَغْطَشَ لَيْلَهَا وَأَخْرَجَ ضُحَاهَا [79:29]

Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.

### الآية 79:30

> ﻿وَالْأَرْضَ بَعْدَ ذَٰلِكَ دَحَاهَا [79:30]

Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.

### الآية 79:31

> ﻿أَخْرَجَ مِنْهَا مَاءَهَا وَمَرْعَاهَا [79:31]

Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.

### الآية 79:32

> ﻿وَالْجِبَالَ أَرْسَاهَا [79:32]

Da duwatsu, Yã kafe ta.

### الآية 79:33

> ﻿مَتَاعًا لَكُمْ وَلِأَنْعَامِكُمْ [79:33]

Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.

### الآية 79:34

> ﻿فَإِذَا جَاءَتِ الطَّامَّةُ الْكُبْرَىٰ [79:34]

To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.

### الآية 79:35

> ﻿يَوْمَ يَتَذَكَّرُ الْإِنْسَانُ مَا سَعَىٰ [79:35]

Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.

### الآية 79:36

> ﻿وَبُرِّزَتِ الْجَحِيمُ لِمَنْ يَرَىٰ [79:36]

Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.

### الآية 79:37

> ﻿فَأَمَّا مَنْ طَغَىٰ [79:37]

To, amma wanda ya yi girman kai.

### الآية 79:38

> ﻿وَآثَرَ الْحَيَاةَ الدُّنْيَا [79:38]

Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).

### الآية 79:39

> ﻿فَإِنَّ الْجَحِيمَ هِيَ الْمَأْوَىٰ [79:39]

To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.

### الآية 79:40

> ﻿وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِ وَنَهَى النَّفْسَ عَنِ الْهَوَىٰ [79:40]

Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.

### الآية 79:41

> ﻿فَإِنَّ الْجَنَّةَ هِيَ الْمَأْوَىٰ [79:41]

To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.

### الآية 79:42

> ﻿يَسْأَلُونَكَ عَنِ السَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَاهَا [79:42]

Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?

### الآية 79:43

> ﻿فِيمَ أَنْتَ مِنْ ذِكْرَاهَا [79:43]

Me ya haɗã ka da ambatonta?

### الآية 79:44

> ﻿إِلَىٰ رَبِّكَ مُنْتَهَاهَا [79:44]

Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.

### الآية 79:45

> ﻿إِنَّمَا أَنْتَ مُنْذِرُ مَنْ يَخْشَاهَا [79:45]

Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.

### الآية 79:46

> ﻿كَأَنَّهُمْ يَوْمَ يَرَوْنَهَا لَمْ يَلْبَثُوا إِلَّا عَشِيَّةً أَوْ ضُحَاهَا [79:46]

Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.

## روابط ذات صلة

- [النص القرآني للسورة](https://quranpedia.net/surah/1/79.md)
- [كل تفاسير سورة النازعات
](https://quranpedia.net/surah-tafsir/79.md)
- [ترجمات سورة النازعات
](https://quranpedia.net/translations/79.md)
- [صفحة الكتاب: الترجمة الهوساوية](https://quranpedia.net/book/1999.md)

---

زُر [Quranpedia.net](https://quranpedia.net/surah/1/79/book/1999) — موسوعة القرآن الكريم: التفاسير، الترجمات، التلاوات، والمواضيع.
