وَأَمَّا مَنۡ أُوتِيَ كِتَٰبَهُۥ بِشِمَالِهِۦ فَيَقُولُ يَٰلَيۡتَنِي لَمۡ أُوتَ كِتَٰبِيَهۡ

Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!"


وَلَمۡ أَدۡرِ مَا حِسَابِيَهۡ

"Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"


يَٰلَيۡتَهَا كَانَتِ ٱلۡقَاضِيَةَ

"In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!


مَآ أَغۡنَىٰ عَنِّي مَالِيَهۡۜ

"Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!"


هَلَكَ عَنِّي سُلۡطَٰنِيَهۡ

"Ĩkona ya ɓace mini!"


خُذُوهُ فَغُلُّوهُ

(Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."


ثُمَّ ٱلۡجَحِيمَ صَلُّوهُ

"Sa'an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."


ثُمَّ فِي سِلۡسِلَةٖ ذَرۡعُهَا سَبۡعُونَ ذِرَاعٗا فَٱسۡلُكُوهُ

"Sa'an nan, acikin sarƙa, tsawonta zirã'i saba'in, sai ku sanya shi."


إِنَّهُۥ كَانَ لَا يُؤۡمِنُ بِٱللَّهِ ٱلۡعَظِيمِ

"Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin ĩmãni da Allah, Mai girma!"



الصفحة التالية
Icon