فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ

Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),


ثُمَّ أَدۡبَرَ يَسۡعَىٰ

Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.


فَحَشَرَ فَنَادَىٰ

Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.


فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلۡأَعۡلَىٰ

Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."


فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلۡأٓخِرَةِ وَٱلۡأُولَىٰٓ

Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.


إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَعِبۡرَةٗ لِّمَن يَخۡشَىٰٓ

Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.


ءَأَنتُمۡ أَشَدُّ خَلۡقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُۚ بَنَىٰهَا

Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.


رَفَعَ سَمۡكَهَا فَسَوَّىٰهَا

Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.


وَأَغۡطَشَ لَيۡلَهَا وَأَخۡرَجَ ضُحَىٰهَا

Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.


وَٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ

Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.



الصفحة التالية
Icon