وَأَمَّا مَنۡ أُوتِيَ كِتَٰبَهُۥ وَرَآءَ ظَهۡرِهِۦ

Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.


فَسَوۡفَ يَدۡعُواْ ثُبُورٗا

To, zã shi dinga kiran halaka!


وَيَصۡلَىٰ سَعِيرًا

Kuma ya shiga sa'ĩr.


إِنَّهُۥ كَانَ فِيٓ أَهۡلِهِۦ مَسۡرُورًا

Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.


إِنَّهُۥ ظَنَّ أَن لَّن يَحُورَ

Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.


بَلَىٰٓۚ إِنَّ رَبَّهُۥ كَانَ بِهِۦ بَصِيرٗا

Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.


فَلَآ أُقۡسِمُ بِٱلشَّفَقِ

To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.


وَٱلَّيۡلِ وَمَا وَسَقَ

Da dare, da abin da ya ƙunsa.


وَٱلۡقَمَرِ إِذَا ٱتَّسَقَ

Da watã idan (haskensa) ya cika.


لَتَرۡكَبُنَّ طَبَقًا عَن طَبَقٖ

Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.


فَمَا لَهُمۡ لَا يُؤۡمِنُونَ

To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?



الصفحة التالية
Icon