إِنَّهُمۡ كَانُوٓاْ إِذَا قِيلَ لَهُمۡ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا ٱللَّهُ يَسۡتَكۡبِرُونَ

Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.


وَيَقُولُونَ أَئِنَّا لَتَارِكُوٓاْ ءَالِهَتِنَا لِشَاعِرٖ مَّجۡنُونِۭ

Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?


بَلۡ جَآءَ بِٱلۡحَقِّ وَصَدَّقَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.


إِنَّكُمۡ لَذَآئِقُواْ ٱلۡعَذَابِ ٱلۡأَلِيمِ

Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.


وَمَا تُجۡزَوۡنَ إِلَّا مَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.


إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلۡمُخۡلَصِينَ

Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.


أُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمۡ رِزۡقٞ مَّعۡلُومٞ

Waɗannan sunã da abinci sananne.


فَوَٰكِهُ وَهُم مُّكۡرَمُونَ

'Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.



الصفحة التالية
Icon