Al-Inshikak


إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنشَقَّتۡ

Idan sama ta kẽce,


وَأَذِنَتۡ لِرَبِّهَا وَحُقَّتۡ

Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,


وَإِذَا ٱلۡأَرۡضُ مُدَّتۡ

Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,


وَأَلۡقَتۡ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتۡ

Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.


وَأَذِنَتۡ لِرَبِّهَا وَحُقَّتۡ

Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,


يَـٰٓأَيُّهَا ٱلۡإِنسَٰنُ إِنَّكَ كَادِحٌ إِلَىٰ رَبِّكَ كَدۡحٗا فَمُلَٰقِيهِ

Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.


فَأَمَّا مَنۡ أُوتِيَ كِتَٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ

To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.


فَسَوۡفَ يُحَاسَبُ حِسَابٗا يَسِيرٗا

To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.


وَيَنقَلِبُ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِۦ مَسۡرُورٗا

Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.



الصفحة التالية
Icon