ﰐ
                    surah.translation
            .
            
    
                                    من تأليف: 
                                            أبو بكر محمود جومي
                                                            .
                                                
            ﰡ
Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta.
                                                                        Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi.
                                                                        Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta?"
                                                                        A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta.
                                                                        cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta.
                                                                        A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu.
                                                                        To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi.
                                                                        Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.