سورة الشمس

الترجمة الهوساوية

د الترجمة الهوساوية څخه په الهوساوية کې د الشمس سورې ژباړه

الترجمة الهوساوية

الناشر

مجمع الملك فهد

Verse 1
Ina rantsuwa da rãnã da hantsinta.
Verse 8
Sa'an nan ya yi masa Ilhamar fãjircinsa da shiryuwarsa.
Verse 9
Lalle ne wanda ya tsarkake* shi (rai) ya sãmi babban rabo.
 * Karɓar imãni da aiki da abinda ya ƙunsa tsarkake rai ne.
Verse 10
Kuma lalle ne wanda ya turbuɗe* shi (da laifi) ya tãɓe.
* Kãfirci turbuɗe rai ne da zunubi.
Verse 11
Samũdãwa sun ƙaryata (Annabinsu), dõmin girman kansu.
Verse 12
A lõkacin da mafi shaƙãwarsu ya tafi (wurin sõke rãkumar sãlihu).
Sai suka ƙaryata shi, sa'an nan suka sõke ta. Sabõda haka Ubangijinsu Ya darkãke su, sabõda zunubinsu. Sa'an nan Ya daidaita ta (azãbar ga mai laifi da maras laifi).
Verse 15
Kuma bã ya tsõron ãƙibarta (ita halakãwar).
تقدم القراءة