سورة الصافات

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Fassarar Surar As-Saffat a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Verse 1

As-Saffat


Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).
Verse 2

Sa'an nan mãsu yin tsãwa dõmin gargaɗi.
Verse 3

Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.
Verse 12

Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.

"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?
Verse 24

Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.

Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."
Verse 32

"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."
Verse 34

Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.

Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?
Verse 38

Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.
Verse 42

'Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.

Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.
Verse 48

Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.
Verse 52

Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"

"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"
Verse 54

(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"

Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."

"Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."

To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.

Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.

Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.
Verse 89

Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."
Verse 90

Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.
Verse 94

Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.
Verse 96

"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"

Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.

Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."
Verse 101

Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro mai haƙuri.
Verse 103

To, a lõkacin da suka yi sallama, (Ibrahĩm) ya kãyar da shi ga gẽfen gõshinsa.
Verse 107

Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.
Verse 112

Kuma Muka yi masa bushãra Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.

Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).
Verse 116

Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.
Verse 117

Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.
Verse 118

Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.
Verse 124

A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"
Verse 125

"Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"
Verse 127

Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).
Verse 129

Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.
Verse 134

A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya.
Verse 135

Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).
Verse 137

Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.
Verse 141

Sã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.
Verse 142

Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
Verse 145

Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.

Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).
Verse 148

Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.
Verse 149

Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"
Verse 152

"Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.

Kuma suka sanya nasaba a tsakãninSa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"
Verse 159

Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.
Verse 165

"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."
Verse 166

"Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."
Verse 169

"Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."
Verse 172

Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.
Verse 175

Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.
Verse 176

Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa?

To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.
Verse 179

Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.

Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.
تقدم القراءة