Fassarar Surar As-Saffat a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
Verse 1
ﭑﭒ
ﭓ
As-Saffat
Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).
Verse 2
ﭔﭕ
ﭖ
Sa'an nan mãsu yin tsãwa dõmin gargaɗi.
Verse 3
ﭗﭘ
ﭙ
Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.
Verse 4
ﭚﭛﭜ
ﭝ
Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.
Verse 5
Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.
Verse 6
ﭦﭧﭨﭩﭪﭫ
ﭬ
Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.
Verse 7
ﭭﭮﭯﭰﭱ
ﭲ
Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.
Verse 8
Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.
Verse 9
ﭽﭾﭿﮀﮁ
ﮂ
Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.
Verse 10
Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.
Verse 11
Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.
Verse 12
ﮙﮚﮛ
ﮜ
Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.
Verse 13
ﮝﮞﮟﮠ
ﮡ
Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.
Verse 14
ﮢﮣﮤﮥ
ﮦ
Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.
Verse 15
ﮧﮨﮩﮪﮫﮬ
ﮭ
Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."
Verse 16
"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?
Verse 17
ﯗﯘ
ﯙ
"Ashe kõ da ubanninmu na farko?"
Verse 18
ﯚﯛﯜﯝ
ﯞ
Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."
Verse 19
Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.
Verse 20
ﯧﯨﯩﯪﯫ
ﯬ
Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."
Verse 21
Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.
Verse 22
Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.
Verse 23
Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.
Verse 24
ﰆﰇﰈﰉ
ﰊ
Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.
Verse 25
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?
Verse 26
ﭖﭗﭘﭙ
ﭚ
Ã'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.
Verse 27
ﭛﭜﭝﭞﭟ
ﭠ
Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.
Verse 28
ﭡﭢﭣﭤﭥﭦ
ﭧ
Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."
Verse 29
ﭨﭩﭪﭫﭬ
ﭭ
Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.
Verse 30
"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."
Verse 31
"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."
Verse 32
ﮂﮃﮄﮅ
ﮆ
"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."
Verse 33
ﮇﮈﮉﮊﮋ
ﮌ
To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.
Verse 34
ﮍﮎﮏﮐ
ﮑ
Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.
Verse 35
Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.
Verse 36
ﮝﮞﮟﮠﮡﮢ
ﮣ
Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?
Verse 37
ﮤﮥﮦﮧﮨ
ﮩ
Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.
Verse 38
ﮪﮫﮬﮭ
ﮮ
Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.
Verse 39
ﮯﮰﮱﯓﯔﯕ
ﯖ
Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
Verse 40
ﯗﯘﯙﯚ
ﯛ
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
Verse 41
ﯜﯝﯞﯟ
ﯠ
Waɗannan sunã da abinci sananne.
Verse 42
ﯡﯢﯣ
ﯤ
'Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.
Verse 43
ﯥﯦﯧ
ﯨ
A cikin gidãjen Aljannar ni'ima.
Verse 44
ﯩﯪﯫ
ﯬ
A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.
Verse 45
ﯭﯮﯯﯰﯱ
ﯲ
Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.
Verse 46
ﯳﯴﯵ
ﯶ
Farã mai dãɗi ga mashãyan.
Verse 47
A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,
Verse 48
ﯿﰀﰁﰂ
ﰃ
Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.
Verse 49
ﰄﰅﰆ
ﰇ
Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.
Verse 50
ﰈﰉﰊﰋﰌ
ﰍ
Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.
Verse 51
Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."
Verse 52
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"
Verse 53
"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"
Verse 54
ﭞﭟﭠﭡ
ﭢ
(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"
Verse 55
ﭣﭤﭥﭦﭧ
ﭨ
Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.
Verse 56
ﭩﭪﭫﭬﭭ
ﭮ
Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."
Verse 57
ﭯﭰﭱﭲﭳﭴ
ﭵ
"Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."
Verse 58
ﭶﭷﭸ
ﭹ
"Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."
Verse 59
ﭺﭻﭼﭽﭾﭿ
ﮀ
"Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"
Verse 60
ﮁﮂﮃﮄﮅ
ﮆ
Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.
Verse 61
ﮇﮈﮉﮊ
ﮋ
Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.
Verse 62
ﮌﮍﮎﮏﮐﮑ
ﮒ
Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?
Verse 63
ﮓﮔﮕﮖ
ﮗ
Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.
Verse 64
ﮘﮙﮚﮛﮜﮝ
ﮞ
Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.
Verse 65
ﮟﮠﮡﮢ
ﮣ
Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.
Verse 66
ﮤﮥﮦﮧﮨﮩ
ﮪ
To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.
Verse 67
Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.
Verse 68
ﯔﯕﯖﯗﯘ
ﯙ
Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.
Verse 69
ﯚﯛﯜﯝ
ﯞ
Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.
Verse 70
ﯟﯠﯡﯢ
ﯣ
Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.
Verse 71
ﯤﯥﯦﯧﯨ
ﯩ
Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.
Verse 72
ﯪﯫﯬﯭ
ﯮ
Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.
Verse 73
ﯯﯰﯱﯲﯳ
ﯴ
Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.
Verse 74
ﯵﯶﯷﯸ
ﯹ
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
Verse 75
ﯺﯻﯼﯽﯾ
ﯿ
Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.
Verse 76
ﰀﰁﰂﰃﰄ
ﰅ
Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.
Verse 77
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.
Verse 78
ﭖﭗﭘﭙ
ﭚ
Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe.
Verse 79
ﭛﭜﭝﭞﭟ
ﭠ
Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.
Verse 80
ﭡﭢﭣﭤ
ﭥ
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
Verse 81
ﭦﭧﭨﭩ
ﭪ
Lalle shi, yanã daga bãyinMu mũminai.
Verse 82
ﭫﭬﭭ
ﭮ
Sã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu.
Verse 83
ﭯﭰﭱﭲﭳ
ﭴ
Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.
Verse 84
ﭵﭶﭷﭸﭹ
ﭺ
A lõkacin da ya je wa dangijinsa da zũciya kuɓutacciya.
Verse 85
ﭻﭼﭽﭾﭿﮀ
ﮁ
A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa?"
Verse 86
ﮂﮃﮄﮅﮆ
ﮇ
"Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"
Verse 87
ﮈﮉﮊﮋ
ﮌ
"To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"
Verse 88
ﮍﮎﮏﮐ
ﮑ
Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.
Verse 89
ﮒﮓﮔ
ﮕ
Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."
Verse 90
ﮖﮗﮘ
ﮙ
Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.
Verse 91
ﮚﮛﮜﮝﮞﮟ
ﮠ
Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?
Verse 92
ﮡﮢﮣﮤ
ﮥ
"Me ya sãme ku, bã ku magana?"
Verse 93
ﮦﮧﮨﮩ
ﮪ
Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.
Verse 94
ﮫﮬﮭ
ﮮ
Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.
Verse 95
ﮯﮰﮱﯓ
ﯔ
Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,
Verse 96
ﯕﯖﯗﯘ
ﯙ
"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"
Verse 97
Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm."
Verse 98
ﯢﯣﯤﯥﯦ
ﯧ
Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.
Verse 99
ﯨﯩﯪﯫﯬﯭ
ﯮ
Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."
Verse 100
ﯯﯰﯱﯲﯳ
ﯴ
"Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."
Verse 101
ﯵﯶﯷ
ﯸ
Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro mai haƙuri.
Verse 102
To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri."
Verse 103
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
To, a lõkacin da suka yi sallama, (Ibrahĩm) ya kãyar da shi ga gẽfen gõshinsa.
Verse 104
ﭖﭗﭘ
ﭙ
Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!"
Verse 105
"Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
Verse 106
ﭣﭤﭥﭦﭧ
ﭨ
Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.
Verse 107
ﭩﭪﭫ
ﭬ
Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.
Verse 108
ﭭﭮﭯﭰ
ﭱ
Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.
Verse 109
ﭲﭳﭴ
ﭵ
Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm.
Verse 110
ﭶﭷﭸ
ﭹ
Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
Verse 111
ﭺﭻﭼﭽ
ﭾ
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
Verse 112
ﭿﮀﮁﮂﮃ
ﮄ
Kuma Muka yi masa bushãra Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.
Verse 113
Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).
Verse 114
ﮑﮒﮓﮔﮕ
ﮖ
Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna.
Verse 115
ﮗﮘﮙﮚﮛ
ﮜ
Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.
Verse 116
ﮝﮞﮟﮠ
ﮡ
Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.
Verse 117
ﮢﮣﮤ
ﮥ
Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.
Verse 118
ﮦﮧﮨ
ﮩ
Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.
Verse 119
ﮪﮫﮬﮭ
ﮮ
Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe.
Verse 120
ﮯﮰﮱﯓ
ﯔ
Aminci ya tabbata ga Mũsã da Hãruna.
Verse 121
ﯕﯖﯗﯘ
ﯙ
Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
Verse 122
ﯚﯛﯜﯝ
ﯞ
Lalle, sunã daga bãyinMu mũminai.
Verse 123
ﯟﯠﯡﯢ
ﯣ
Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
Verse 124
ﯤﯥﯦﯧﯨ
ﯩ
A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"
Verse 125
ﯪﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
"Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"
Verse 126
ﯰﯱﯲﯳﯴ
ﯵ
"Allah Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku farko?"
Verse 127
ﭑﭒﭓ
ﭔ
Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).
Verse 128
ﭕﭖﭗﭘ
ﭙ
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
Verse 129
ﭚﭛﭜﭝ
ﭞ
Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.
Verse 130
ﭟﭠﭡﭢ
ﭣ
Aminci ya tabbata ga Ilyãs.
Verse 131
ﭤﭥﭦﭧ
ﭨ
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
Verse 132
ﭩﭪﭫﭬ
ﭭ
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
Verse 133
ﭮﭯﭰﭱ
ﭲ
Kuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
Verse 134
ﭳﭴﭵﭶ
ﭷ
A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya.
Verse 135
ﭸﭹﭺﭻ
ﭼ
Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).
Verse 136
ﭽﭾﭿ
ﮀ
Sã'an nan Muka darkãke waɗansu mutãnen.
Verse 137
ﮁﮂﮃﮄ
ﮅ
Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.
Verse 138
ﮆﮇﮈﮉ
ﮊ
Kuma da dare. Shin fa, bã zã ku hankalta ba?
Verse 139
ﮋﮌﮍﮎ
ﮏ
Kuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
Verse 140
ﮐﮑﮒﮓﮔ
ﮕ
A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi.
Verse 141
ﮖﮗﮘﮙ
ﮚ
Sã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.
Verse 142
ﮛﮜﮝﮞ
ﮟ
Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
Verse 143
ﮠﮡﮢﮣﮤ
ﮥ
To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba,
Verse 144
ﮦﮧﮨﮩﮪﮫ
ﮬ
Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.
Verse 145
ﮭﮮﮯﮰﮱ
ﯓ
Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.
Verse 146
ﯔﯕﯖﯗﯘ
ﯙ
Kuma Muka tsirar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi.
Verse 147
ﯚﯛﯜﯝﯞﯟ
ﯠ
Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).
Verse 148
ﯡﯢﯣﯤ
ﯥ
Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.
Verse 149
ﯦﯧﯨﯩﯪ
ﯫ
Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"
Verse 150
ﯬﯭﯮﯯﯰﯱ
ﯲ
Kõ kuma Mun halitta malã'iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce?
Verse 151
ﯳﯴﯵﯶﯷ
ﯸ
To! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cẽwa.
Verse 152
ﯹﯺﯻﯼ
ﯽ
"Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.
Verse 153
ﯾﯿﰀﰁ
ﰂ
Shin, Yã zãɓi 'yã'ya mãtã ne a kan ɗiya maza?
Verse 154
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannanhukunci)?
Verse 155
ﭖﭗ
ﭘ
Shin, bã ku tunãni?
Verse 156
ﭙﭚﭛﭜ
ﭝ
Ko kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne?
Verse 157
ﭞﭟﭠﭡﭢ
ﭣ
To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.
Verse 158
Kuma suka sanya nasaba a tsakãninSa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"
Verse 159
ﭰﭱﭲﭳ
ﭴ
Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.
Verse 160
ﭵﭶﭷﭸ
ﭹ
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
Verse 161
ﭺﭻﭼ
ﭽ
To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,
Verse 162
ﭾﭿﮀﮁ
ﮂ
Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi.
Verse 163
ﮃﮄﮅﮆﮇ
ﮈ
Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.
Verse 164
ﮉﮊﮋﮌﮍﮎ
ﮏ
"Kuma bãbu kõwa daga cikinmu, fãce yanã da matsayi sananne."
Verse 165
ﮐﮑﮒ
ﮓ
"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."
Verse 166
ﮔﮕﮖ
ﮗ
"Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."
Verse 167
ﮘﮙﮚ
ﮛ
Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa,
Verse 168
ﮜﮝﮞﮟﮠﮡ
ﮢ
"Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko."
Verse 169
ﮣﮤﮥﮦ
ﮧ
"Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."
Verse 170
ﮨﮩﮪﮫﮬ
ﮭ
Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani.
Verse 171
ﮮﮯﮰﮱﯓ
ﯔ
Kuma lalle, haƙĩƙa kalmarMu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.
Verse 172
ﯕﯖﯗ
ﯘ
Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.
Verse 173
ﯙﯚﯛﯜ
ﯝ
Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.
Verse 174
ﯞﯟﯠﯡ
ﯢ
Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.
Verse 175
ﯣﯤﯥ
ﯦ
Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.
Verse 176
ﯧﯨ
ﯩ
Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa?
Verse 177
ﯪﯫﯬﯭﯮﯯ
ﯰ
To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.
Verse 178
ﯱﯲﯳﯴ
ﯵ
Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci.
Verse 179
ﯶﯷﯸ
ﯹ
Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.
Verse 180
ﯺﯻﯼﯽﯾﯿ
ﰀ
Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.
Verse 181
ﰁﰂﰃ
ﰄ
Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni.
Verse 182
ﰅﰆﰇﰈ
ﰉ
Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.
تقدم القراءة