Fassarar Surar An-Takwir a الهوساوية daga الترجمة الهوساوية
Verse 1
ﭙﭚﭛ
ﭜ
Idan rãna aka shafe haskenta
Verse 2
ﭝﭞﭟ
ﭠ
Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).
Verse 3
ﭡﭢﭣ
ﭤ
Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.
Verse 4
ﭥﭦﭧ
ﭨ
Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna* aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.
* Rãƙuma mãsu ciki ɗan wata gõma.
Verse 5
ﭩﭪﭫ
ﭬ
Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.
Verse 6
ﭭﭮﭯ
ﭰ
Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.
Verse 7
ﭱﭲﭳ
ﭴ
Kuma idan rãyuka aka haɗa* su da jikunkunansu.
* Ko kuma, aka haɗa kõwane mutum da irin mutãnensa a Aljanna ko a wuta.
Verse 8
ﭵﭶﭷ
ﭸ
Kuma idan wadda aka turbuɗe* ta da rai aka tambaye ta.
* A cikin zãmanin jahiliyya Lãrabãwa bã su son a haifa musu 'ya'ya mãta dõmin haka har sukan turbuɗe 'ya'yansu dõmin kada su yi abin kunya ko kuma su talauce wajen yi musu aure.
Verse 9
ﭹﭺﭻ
ﭼ
"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"
Verse 10
ﭽﭾﭿ
ﮀ
Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).
Verse 11
ﮁﮂﮃ
ﮄ
Kuma idan sama aka fẽɗe ta.
Verse 12
ﮅﮆﮇ
ﮈ
Kuma idan Jahĩm aka hũra ta
Verse 13
ﮉﮊﮋ
ﮌ
Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.
Verse 14
ﮍﮎﮏﮐ
ﮑ
Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).
Verse 15
ﮒﮓﮔ
ﮕ
To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã* ba.
* Masu tafiya suna kõmawa bãya.
Verse 16
ﮖﮗ
ﮘ
Mãsu gudu suna ɓũya.
Verse 17
ﮙﮚﮛ
ﮜ
Da dare idan ya bãyar da bãya.
Verse 18
ﮝﮞﮟ
ﮠ
Da sãfiya idan ta yi lumfashi.
Verse 19
ﮡﮢﮣﮤ
ﮥ
Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.
Verse 20
ﮦﮧﮨﮩﮪﮫ
ﮬ
Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.
Verse 21
ﮭﮮﮯ
ﮰ
Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.
Verse 22
ﮱﯓﯔ
ﯕ
Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.
Verse 23
ﯖﯗﯘﯙ
ﯚ
Kuma lalle ne, yã gan shi(5) a cikin sararin sama mabayyani.
(5) Annabi ya ga Mala'ika Jibirilu ya san shi. Sabõda haka wani aljani bã zai yi kama da shi ba balle ya kãwo masa ƙarya.
Verse 24
ﯛﯜﯝﯞﯟ
ﯠ
Kuma shi, ga gaibi(6) bã mai rowa ba ne.
(6) Ma'anar gaibi a nan, ilmin da Allah Ya aiko Jibirilu da shi zuwa ga Annabi Annabi ba ya ɓõye shi daga mutãne. Ga wata ƙira'a, wanda ake tuhuma, wãto ba a tuhumar Annabi, ga gaibin da ya faɗi cewa daga Allah yake, wato Alƙur'ãni duka gaskiya ne.
Verse 25
ﯡﯢﯣﯤﯥ
ﯦ
Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.
Verse 26
ﯧﯨ
ﯩ
Shin, a inã zã ku tafi?
Verse 27
ﯪﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.
Verse 28
ﯰﯱﯲﯳﯴ
ﯵ
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.
Verse 29
Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.
تقدم القراءة