سورة الواقعة

الترجمة الهوساوية

Fassarar Surar Al-Waki'ah a الهوساوية daga الترجمة الهوساوية

الترجمة الهوساوية

الناشر

مجمع الملك فهد

Verse 3
(Ita) mai ƙasƙantãwa ce, mai ɗaukakãwa.
Watau mazõwa dãma*. Mẽne ne mazõwa dãma?
____________________
 * Mazõwa dãma ko mãsu albarka waɗanda zã a baiwa takardunsu a dãma. Mazõwa hagu ko mãsu shu'umci waɗanda zã a baiwa takardunsu da hagu.
Verse 10
Da waɗanda suka tsẽre. Sũ wɗanda suka tsẽren nan,
Verse 11
Waɗancan, sũ ne waɗanda aka kusantar.
Verse 13
Jama'a ne daga mutãnen farko.*
____________________
   * Jama'a daga mutãnen farko, sũ ne Annabãwan farko da kaɗan daga cikin mutãnen ƙarshe, shi ne Annabi Muhammadu, sallallãhu alaihi wa sallama. Bã a shiga cikin wannan kashi da aiki sai dai da zãɓin Allah. Kuma an rufe ƙõfarsa. Bãbu sauran wani annabi wanda zai zo da wani addini sãbo a bãyan Annabi Muhammadu, tsĩra da amincin Allah su tabbata a gare shi.
Verse 16
Sunã gincire a kansu, sunã mãsu kallon jũna.
Verse 20
Da wasu 'ya'yan itãcen marmari daga irin waɗanda suke zãɓe.
Verse 22
Da wasu mãtã mãsu fararen idanu da girmansu.
Verse 24
A kan sakamakon, dõmin abin da suka kasance sunã aikatãwa.
Verse 32
Da wasu 'ya'yan itacen marmari mãsu yawa.
Verse 37
Mãsu son mazansu, a cikin tsãrã ɗaya.
Verse 42
Sunã a cikin wata iskar zãfi da wani ruwan zãfi.
Kuma sun kasance sunã cẽwa: "Shin idan mun mutukuma muko kasance turɓãya da ƙasũsuwa shin lalle mũ waɗanda zã a kõma rãyarwa ne haƙĩƙatan?"
Verse 48
"Shin, kuma da ubanninmu na farko?"
Verse 53
"Har za ku zama mãsu cika cikunna daga gare ta."
Verse 54
"Sa'an nan kuma mãsu shã ne, a kan wannan abin cin, daga ruwan zãfi."
Verse 55
"Ku zama mãsu shã irin shan rãƙuma mãsu ƙishirwa."
Verse 58
Shin kuma kun ga abin da kuke fitarwa na maniyyi?
Mũ ne Muka ƙaddara mutuwa a tsakãninku, kuma ba Mu zama Mãsu gajiyãwa* ba,
____________________
  * Ãyã ta 60 haɗe take da ãya ta 61 watau, bã zã Mu kãsa musanya ku da waɗansu mutãne ba su tsaya matsayinku, sa'an nan kũ kuma Mu mayar da ku wata halitta.
Kuma lalle, ne haƙĩƙa, kun san halittar farko, to, don me ba zã ku yi tunãni ba?
Dã Munã so lalle, da Mun sanya shi bũsasshiyar ciyãwa, sai ku yini kunã mãmãkin bãƙin ciki.
Verse 66
(Kunã cẽwa) "Lalle haƙĩƙa an azã mana tãra!"
Mũ ne Muka sanya ta wata abar wa'azi da jin dãɗi ga matafiya a cikin jẽji.
Verse 77
Lalle shi (wannan littãfi), haƙĩƙa, abin karantãwa ne mai daraja.
Verse 82
Kuma kunã sanya arzikinku (game da shi) lalle kũ, ku ƙaryata (shi)?
Verse 83
To, don me idan rai ya kai ga maƙõshi? (Kusa da mutuwa).
Verse 84
Alhãli kuwa kũ, a lõklcin nan, kunã kallo.
Verse 87
Ku mayar da shi (cikin jikinsa) har idan kun kasance mãsu gaskiya.*
____________________
 * Idan kun kasance mãsu gaskiya ga da'awar rashin Tãshin Ƙiyãma, to, ku yi ƙõƙarin hana mutuwa ga mutãne dõmin ku hana cikar alkawarin tayarwa a bãyan mutuwa.
Verse 96
Sabõda haka, ka tsarkake* sũnan Ubangijinka, Mai karimci.
____________________
 * A cikin rukũ'i anã tasbĩhi da cewa: "Subhãna Rabbiyal Azĩm wa Bihamdih." Ma'anarsa Tsarki ya tabbata ga Ubangijina Mai girma game da gõde Masa.
تقدم القراءة