Fassarar Surar Al-Waki'ah a الهوساوية daga الترجمة الهوساوية
Verse 1
ﮃﮄﮅ
ﮆ
Idan mai aukuwa ta auku.
Verse 2
ﮇﮈﮉ
ﮊ
Bãbu wani (rai) mai ƙaryatãwa ga aukuwarta.
Verse 3
ﮋﮌ
ﮍ
(Ita) mai ƙasƙantãwa ce, mai ɗaukakãwa.
Verse 4
ﮎﮏﮐﮑ
ﮒ
Idan aka girgiza ƙasã girgizwa.
Verse 5
ﮓﮔﮕ
ﮖ
Kuma aka niƙe duwãtsu, niƙẽwa.
Verse 6
ﮗﮘﮙ
ﮚ
Sai suka kasance ƙũra da ake wãtsarwa.
Verse 7
ﮛﮜﮝ
ﮞ
Kuma kun kasance nau'i uku.
Verse 8
ﮟﮠﮡﮢﮣ
ﮤ
Watau mazõwa dãma*. Mẽne ne mazõwa dãma?
____________________
* Mazõwa dãma ko mãsu albarka waɗanda zã a baiwa takardunsu a dãma. Mazõwa hagu ko mãsu shu'umci waɗanda zã a baiwa takardunsu da hagu.
____________________
* Mazõwa dãma ko mãsu albarka waɗanda zã a baiwa takardunsu a dãma. Mazõwa hagu ko mãsu shu'umci waɗanda zã a baiwa takardunsu da hagu.
Verse 9
ﮥﮦﮧﮨﮩ
ﮪ
Da mazõwa hagu. Mẽne ne mazõwa hagu?
Verse 10
ﮫﮬ
ﮭ
Da waɗanda suka tsẽre. Sũ wɗanda suka tsẽren nan,
Verse 11
ﮮﮯ
ﮰ
Waɗancan, sũ ne waɗanda aka kusantar.
Verse 12
ﮱﯓﯔ
ﯕ
A ckin Aljannar ni'ima.
Verse 13
ﯖﯗﯘ
ﯙ
Jama'a ne daga mutãnen farko.*
____________________
* Jama'a daga mutãnen farko, sũ ne Annabãwan farko da kaɗan daga cikin mutãnen ƙarshe, shi ne Annabi Muhammadu, sallallãhu alaihi wa sallama. Bã a shiga cikin wannan kashi da aiki sai dai da zãɓin Allah. Kuma an rufe ƙõfarsa. Bãbu sauran wani annabi wanda zai zo da wani addini sãbo a bãyan Annabi Muhammadu, tsĩra da amincin Allah su tabbata a gare shi.
____________________
* Jama'a daga mutãnen farko, sũ ne Annabãwan farko da kaɗan daga cikin mutãnen ƙarshe, shi ne Annabi Muhammadu, sallallãhu alaihi wa sallama. Bã a shiga cikin wannan kashi da aiki sai dai da zãɓin Allah. Kuma an rufe ƙõfarsa. Bãbu sauran wani annabi wanda zai zo da wani addini sãbo a bãyan Annabi Muhammadu, tsĩra da amincin Allah su tabbata a gare shi.
Verse 14
ﯚﯛﯜ
ﯝ
Da kaɗan daga mutãnen ƙarshe.
Verse 15
ﯞﯟﯠ
ﯡ
(Sunã) a kan wasu gadãje sãƙaƙƙuu.
Verse 16
ﯢﯣﯤ
ﯥ
Sunã gincire a kansu, sunã mãsu kallon jũna.
Verse 17
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
Wasu yara samãri na dindindin gẽwaya a kansu.
Verse 18
ﭖﭗﭘﭙﭚ
ﭛ
Da wasu kõfuna da shantula da hinjãlai daga (giya) mai ɓuɓɓuga.
Verse 19
ﭜﭝﭞﭟﭠ
ﭡ
Bã a sanya musu cĩwon jirĩ sabõda ita, kuma bã su buguwa.
Verse 20
ﭢﭣﭤ
ﭥ
Da wasu 'ya'yan itãcen marmari daga irin waɗanda suke zãɓe.
Verse 21
ﭦﭧﭨﭩ
ﭪ
Da nãman tsuntsãye daga wanda suke ganin sha'awa.
Verse 22
ﭫﭬ
ﭭ
Da wasu mãtã mãsu fararen idanu da girmansu.
Verse 23
ﭮﭯﭰ
ﭱ
Kamar misãlan lu'ulu'u wanda aka ɓõye.
Verse 24
ﭲﭳﭴﭵ
ﭶ
A kan sakamakon, dõmin abin da suka kasance sunã aikatãwa.
Verse 25
ﭷﭸﭹﭺﭻﭼ
ﭽ
Bã su jin wata yãsassar magana a cikinta, kuma bã su jin sun yi laifi.
Verse 26
ﭾﭿﮀﮁ
ﮂ
Sai dai wata magana (mai dãɗi): Salãmun, Salãmun.
Verse 27
ﮃﮄﮅﮆﮇ
ﮈ
Da mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?
Verse 28
ﮉﮊﮋ
ﮌ
(Sunã) a cikin itãcen magarya maras ƙaya.
Verse 29
ﮍﮎ
ﮏ
Da wata ayaba mai yawan 'ya'ya.
Verse 30
ﮐﮑ
ﮒ
Da wata inuwa mĩƙaƙƙiya.
Verse 31
ﮓﮔ
ﮕ
Da wani ruwa mai gudãna.
Verse 32
ﮖﮗ
ﮘ
Da wasu 'ya'yan itacen marmari mãsu yawa.
Verse 33
ﮙﮚﮛﮜ
ﮝ
Bã su yankẽwa kuma bã a hana su.
Verse 34
ﮞﮟ
ﮠ
Da wasu shimfiɗu maɗaukaka.
Verse 35
ﮡﮢﮣ
ﮤ
Lalle Mũ, Mun ƙãga halittarsu ƙãgãwa.
Verse 36
ﮥﮦ
ﮧ
Sa'an nan Muka sanya su budurwai.
Verse 37
ﮨﮩ
ﮪ
Mãsu son mazansu, a cikin tsãrã ɗaya.
Verse 38
ﮫﮬ
ﮭ
Ga mazõwa dãma.
Verse 39
ﮮﮯﮰ
ﮱ
Wata ƙungiya ce daga mutãnen farko.
Verse 40
ﯓﯔﯕ
ﯖ
Da wata ƙungiya daga mutãnen ƙarshe.
Verse 41
ﯗﯘﯙﯚﯛ
ﯜ
Mazõwa hagu, Mẽne ne mazõwa hagu?
Verse 42
ﯝﯞﯟ
ﯠ
Sunã a cikin wata iskar zãfi da wani ruwan zãfi.
Verse 43
ﯡﯢﯣ
ﯤ
Da wata inuwa ta hayãƙi mai baƙi.
Verse 44
ﯥﯦﯧﯨ
ﯩ
Bã mai sanyi ba, kuma bã mai wata ni'ima ba.
Verse 45
ﯪﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
Lalle sũ, sun kasance a gabãnin wannan waɗanda aka jiyar dãɗi.
Verse 46
ﯰﯱﯲﯳﯴ
ﯵ
Kuma sun kasance sunã dõgẽwa a kan mummũnan zunubi mai girma.
Verse 47
Kuma sun kasance sunã cẽwa: "Shin idan mun mutukuma muko kasance turɓãya da ƙasũsuwa shin lalle mũ waɗanda zã a kõma rãyarwa ne haƙĩƙatan?"
Verse 48
ﰀﰁ
ﰂ
"Shin, kuma da ubanninmu na farko?"
Verse 49
ﰃﰄﰅﰆ
ﰇ
Ka ce: "Lalle mutãnen farko da na ƙarshe."
Verse 50
ﰈﰉﰊﰋﰌ
ﰍ
"Tabbas, waɗanda ake tãrãwa ne a cikin wani yini sananne."
Verse 51
ﭑﭒﭓﭔﭕ
ﭖ
"Sa'an nan lalle ku, ya kũ ɓatattu, mãsu ƙaryatãwa!"
Verse 52
ﭗﭘﭙﭚﭛ
ﭜ
"Lalle mãsu cĩ ne daga wata itãciya ta zaƙƙum (ɗanyen wutã)."
Verse 53
ﭝﭞﭟ
ﭠ
"Har za ku zama mãsu cika cikunna daga gare ta."
Verse 54
ﭡﭢﭣﭤ
ﭥ
"Sa'an nan kuma mãsu shã ne, a kan wannan abin cin, daga ruwan zãfi."
Verse 55
ﭦﭧﭨ
ﭩ
"Ku zama mãsu shã irin shan rãƙuma mãsu ƙishirwa."
Verse 56
ﭪﭫﭬﭭ
ﭮ
Wannan ita ce liyãfarsu a rãnar sakamako.
Verse 57
ﭯﭰﭱﭲ
ﭳ
Mũ ne Muka halitta ku, to, don me bã zã ku gaskata ba?
Verse 58
ﭴﭵﭶ
ﭷ
Shin kuma kun ga abin da kuke fitarwa na maniyyi?
Verse 59
ﭸﭹﭺﭻﭼ
ﭽ
Shin kũ ne kuke halitta shi, kõ kuwa mũ ne Mãsu halittãwa?
Verse 60
Mũ ne Muka ƙaddara mutuwa a tsakãninku, kuma ba Mu zama Mãsu gajiyãwa* ba,
____________________
* Ãyã ta 60 haɗe take da ãya ta 61 watau, bã zã Mu kãsa musanya ku da waɗansu mutãne ba su tsaya matsayinku, sa'an nan kũ kuma Mu mayar da ku wata halitta.
____________________
* Ãyã ta 60 haɗe take da ãya ta 61 watau, bã zã Mu kãsa musanya ku da waɗansu mutãne ba su tsaya matsayinku, sa'an nan kũ kuma Mu mayar da ku wata halitta.
Verse 61
A kan Mu musanya waɗansu (mutãne) kamarku, kuma Mu mayar da ku a cikin wata halitta da ba ku sani ba.
Verse 62
ﮐﮑﮒﮓﮔﮕ
ﮖ
Kuma lalle, ne haƙĩƙa, kun san halittar farko, to, don me ba zã ku yi tunãni ba?
Verse 63
ﮗﮘﮙ
ﮚ
Shin, kuma kun ga abin da kũke nõmãwa?
Verse 64
ﮛﮜﮝﮞﮟ
ﮠ
Shin, kũ ne ke tsirar da shi kõ kuwa Mũ ne Mãsu tsirarwa?
Verse 65
ﮡﮢﮣﮤﮥﮦ
ﮧ
Dã Munã so lalle, da Mun sanya shi bũsasshiyar ciyãwa, sai ku yini kunã mãmãkin bãƙin ciki.
Verse 66
ﮨﮩ
ﮪ
(Kunã cẽwa) "Lalle haƙĩƙa an azã mana tãra!"
Verse 67
ﮫﮬﮭ
ﮮ
"Ã'a, mun dai zama waɗanda aka hanã wa!"
Verse 68
ﮯﮰﮱﯓ
ﯔ
Shin, kuma kun ga ruwa wannan da kuke sha?
Verse 69
Shin, kũ ne kuke saukar da shi daga girgije, kõ kuwa Mũne Mãsu saukarwa?
Verse 70
ﯝﯞﯟﯠﯡﯢ
ﯣ
Dã Mun so, dã Mun mayar da shi ruwan zartsi. To don me bã ku gõdẽwa?
Verse 71
ﯤﯥﯦﯧ
ﯨ
Shin, kuma kun ga wutã wannan da kuke ƙyastãwa?
Verse 72
ﯩﯪﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
Shin, kũ ne kuke ƙagã halittar itãciyarta, kõ kuwa Mũ ne Mãsu ƙãgãwa?
Verse 73
ﯰﯱﯲﯳﯴ
ﯵ
Mũ ne Muka sanya ta wata abar wa'azi da jin dãɗi ga matafiya a cikin jẽji.
Verse 74
ﯶﯷﯸﯹ
ﯺ
Sai ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mai girma.
Verse 75
ﯻﯼﯽﯾﯿ
ﰀ
To, bã sai Na yi rantsuwa ba da lõkutan fãɗuwar taurãri.
Verse 76
ﰁﰂﰃﰄﰅ
ﰆ
Kuma lalle ne' haƙĩƙa, rantsuwa ce mai girma, dã kun sani.
Verse 77
ﭑﭒﭓ
ﭔ
Lalle shi (wannan littãfi), haƙĩƙa, abin karantãwa ne mai daraja.
Verse 78
ﭕﭖﭗ
ﭘ
A cikin wani littafi tsararre.
Verse 79
ﭙﭚﭛﭜ
ﭝ
Bãbu mai shãfa shi fãce waɗanda aka tsarkake.
Verse 80
ﭞﭟﭠﭡ
ﭢ
Wanda aka saukar ne daga Ubangijin halitta.
Verse 81
ﭣﭤﭥﭦ
ﭧ
Shin, to, wannan lãbãrin ne kuke mãsu wulãkantãwa?
Verse 82
ﭨﭩﭪﭫ
ﭬ
Kuma kunã sanya arzikinku (game da shi) lalle kũ, ku ƙaryata (shi)?
Verse 83
ﭭﭮﭯﭰ
ﭱ
To, don me idan rai ya kai ga maƙõshi? (Kusa da mutuwa).
Verse 84
ﭲﭳﭴ
ﭵ
Alhãli kuwa kũ, a lõklcin nan, kunã kallo.
Verse 85
Kuma Mũ ne mafi kusanta gare shi daga gare ku, to, amma kũ bã ku gani.
Verse 86
ﭾﭿﮀﮁﮂ
ﮃ
To, don me in dai kun kasance bã waɗanda zã a yi wa sakamako ba?
Verse 87
ﮄﮅﮆﮇ
ﮈ
Ku mayar da shi (cikin jikinsa) har idan kun kasance mãsu gaskiya.*
____________________
* Idan kun kasance mãsu gaskiya ga da'awar rashin Tãshin Ƙiyãma, to, ku yi ƙõƙarin hana mutuwa ga mutãne dõmin ku hana cikar alkawarin tayarwa a bãyan mutuwa.
____________________
* Idan kun kasance mãsu gaskiya ga da'awar rashin Tãshin Ƙiyãma, to, ku yi ƙõƙarin hana mutuwa ga mutãne dõmin ku hana cikar alkawarin tayarwa a bãyan mutuwa.
Verse 88
ﮉﮊﮋﮌﮍ
ﮎ
To, amma idan (mai mutuwar) ya kasance daga makusanta,
Verse 89
ﮏﮐﮑﮒ
ﮓ
Sai hũtawa da kyakkyawan abinci da Aljannar ni'ima.
Verse 90
ﮔﮕﮖﮗﮘﮙ
ﮚ
Kuma amma idan ya kasance daga mazõwa dãma,
Verse 91
ﮛﮜﮝﮞﮟ
ﮠ
Sai (a ce masa) aminci ya tabbata a gare ka daga mazõwa dãma.
Verse 92
ﮡﮢﮣﮤﮥﮦ
ﮧ
Kuma amma idan ya kasance daga mãsu ƙaryatãwar, ɓatattun,
Verse 93
ﮨﮩﮪ
ﮫ
Sai wata liyãfa ta ruwan zãfi.
Verse 94
ﮬﮭ
ﮮ
Da ƙõnuwa da Jahĩm,
Verse 95
ﮯﮰﮱﯓﯔ
ﯕ
Lalle wannan, haƙĩƙa, ita ce gaskiya ta yaƙĩni.
Verse 96
ﯖﯗﯘﯙ
ﯚ
Sabõda haka, ka tsarkake* sũnan Ubangijinka, Mai karimci.
____________________
* A cikin rukũ'i anã tasbĩhi da cewa: "Subhãna Rabbiyal Azĩm wa Bihamdih." Ma'anarsa Tsarki ya tabbata ga Ubangijina Mai girma game da gõde Masa.
____________________
* A cikin rukũ'i anã tasbĩhi da cewa: "Subhãna Rabbiyal Azĩm wa Bihamdih." Ma'anarsa Tsarki ya tabbata ga Ubangijina Mai girma game da gõde Masa.
تقدم القراءة