Fassarar Surar Al-Kalam a الهوساوية daga الترجمة الهوساوية
Verse 1
ﮉﮊﮋﮌﮍ
ﮎ
Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.
Verse 2
ﮏﮐﮑﮒﮓ
ﮔ
Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.
Verse 3
ﮕﮖﮗﮘﮙ
ﮚ
Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.
Verse 4
ﮛﮜﮝﮞ
ﮟ
Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.
Verse 5
ﮠﮡ
ﮢ
Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.
Verse 6
ﮣﮤ
ﮥ
Ga wanenku haukã take.
Verse 7
Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkinSa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.
Verse 8
ﯓﯔﯕ
ﯖ
Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.
Verse 9
ﯗﯘﯙﯚ
ﯛ
Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.
Verse 10
ﯜﯝﯞﯟﯠ
ﯡ
Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.
Verse 11
ﯢﯣﯤ
ﯥ
Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.
Verse 12
ﯦﯧﯨﯩ
ﯪ
Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.
Verse 13
ﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).
Verse 14
ﯰﯱﯲﯳﯴ
ﯵ
Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.
Verse 15
Idan ana karanta masa ãyõyinMu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."
Verse 16
ﯾﯿﰀ
ﰁ
Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.
Verse 17
Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.
Verse 18
ﭜﭝ
ﭞ
Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.
Verse 19
Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.
Verse 20
ﭧﭨ
ﭩ
Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.
Verse 21
ﭪﭫ
ﭬ
Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.
Verse 22
Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa.
Verse 23
ﭵﭶﭷ
ﭸ
Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).
Verse 24
ﭹﭺﭻﭼﭽﭾ
ﭿ
"Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!"
Verse 25
ﮀﮁﮂﮃ
ﮄ
Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.
Verse 26
ﮅﮆﮇﮈﮉ
ﮊ
Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"
Verse 27
ﮋﮌﮍ
ﮎ
"Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne."
Verse 28
Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"
Verse 29
ﮗﮘﮙﮚﮛﮜ
ﮝ
Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."
Verse 30
ﮞﮟﮠﮡﮢ
ﮣ
Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu.
Verse 31
ﮤﮥﮦﮧﮨ
ﮩ
Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka."
Verse 32
"Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne."
Verse 33
Haka dai azãbar* take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã.
____________________
* Irin wannan azãba ce za a yi wa Ƙuraishãwa, dangin Annabi, kamar yadda aka yi wa mãsu gonar lambu, wãto da suka tũba aka musanya musu da abin da ya fi abin da suka sãba sãmu. Wato an gayã wa Annabi ne lõkacin da danginsa suka kangare, suka ƙi shiga Musulunci, aka yi musu azãbar fari, da rashin ruwa shekara bakwai, Allah Ya gaya masa cewa, zã su musulunta, alheri ya kõma musu. Ya kuwa kõma, kamar yadda Allah Ya yi alkawari
____________________
* Irin wannan azãba ce za a yi wa Ƙuraishãwa, dangin Annabi, kamar yadda aka yi wa mãsu gonar lambu, wãto da suka tũba aka musanya musu da abin da ya fi abin da suka sãba sãmu. Wato an gayã wa Annabi ne lõkacin da danginsa suka kangare, suka ƙi shiga Musulunci, aka yi musu azãbar fari, da rashin ruwa shekara bakwai, Allah Ya gaya masa cewa, zã su musulunta, alheri ya kõma musu. Ya kuwa kõma, kamar yadda Allah Ya yi alkawari
Verse 34
ﯡﯢﯣﯤﯥﯦ
ﯧ
Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima.
Verse 35
ﯨﯩﯪ
ﯫ
Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi?
Verse 36
ﯬﯭﯮﯯ
ﯰ
Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)?
Verse 37
ﯱﯲﯳﯴﯵ
ﯶ
Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa?
Verse 38
ﯷﯸﯹﯺﯻ
ﯼ
Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa?
Verse 39
Kõ kunã (riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kanMu, har ya zuwa Rãnar ¡iyãma, cẽwa lalle ne kunã da abin da kuke hukuntã wa kanku?
Verse 40
ﰊﰋﰌﰍ
ﰎ
Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)?
Verse 41
Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya.
Verse 42
Ranar da zã a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujũda, sai bã zã su iyãwa ba.
Verse 43
Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi).
Verse 44
Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna lãbãri (Alƙur'ãni). Zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba.
Verse 45
ﭪﭫﭬﭭﭮﭯ
ﭰ
Ina jinkirtã musu, lalle kaidiNa mai ƙarfi ne.
Verse 46
Kõ kana tambayar su wata la'ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu?
Verse 47
ﭹﭺﭻﭼﭽ
ﭾ
Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne?
Verse 48
Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.
Verse 49
Ba dõmin ni'ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi.
Verse 50
ﮖﮗﮘﮙﮚ
ﮛ
Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki.
Verse 51
Kuma lalle, ne waɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da kallonsu (kallon mãmãki), a lokacin da suke jin karãtun Alƙur'ãni, kuma sunã cẽwa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!"
Verse 52
ﮩﮪﮫﮬﮭ
ﮮ
Shi (Alƙur'ãni) bai kasance ba, fãce abin tunãtarwa ne ga duka dũniya.
تقدم القراءة