سورة النازعات

الترجمة الهوساوية

Fassarar Surar An-Nazi'at a الهوساوية daga الترجمة الهوساوية

الترجمة الهوساوية

الناشر

مجمع الملك فهد

Verse 1
Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.
Verse 2
Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.
Verse 3
Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.
Verse 4
Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.
Verse 5
Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.
Verse 6
Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.
Verse 7
Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.
Verse 8
Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.
Verse 9
Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.
Verse 19
"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"
Verse 20
Sai ya nũna masa ãyar* nan mafi girma.
____________________
 * Ãyar Mũsã da ta fi girma ita ce sandarsa mai zama maciji ko hannunsa mai haske kamar tõcila idan yã sanya cikin hammata yã fitar.
Verse 21
Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
Verse 22
Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
Verse 23
Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.
Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
Verse 28
Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.
Verse 33
Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.
Verse 38
Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).
Verse 44
Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.
تقدم القراءة