Fassarar Surar An-Nazi'at a الهوساوية daga الترجمة الهوساوية
Verse 1
ﮢﮣ
ﮤ
Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.
Verse 2
ﮥﮦ
ﮧ
Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.
Verse 3
ﮨﮩ
ﮪ
Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.
Verse 4
ﮫﮬ
ﮭ
Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.
Verse 5
ﮮﮯ
ﮰ
Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.
Verse 6
ﮱﯓﯔ
ﯕ
Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.
Verse 7
ﯖﯗ
ﯘ
Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.
Verse 8
ﯙﯚﯛ
ﯜ
Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.
Verse 9
ﯝﯞ
ﯟ
Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.
Verse 10
ﯠﯡﯢﯣﯤ
ﯥ
Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?
Verse 11
ﯦﯧﯨﯩ
ﯪ
"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"
Verse 12
ﯫﯬﯭﯮﯯ
ﯰ
Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"
Verse 13
ﯱﯲﯳﯴ
ﯵ
To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.
Verse 14
ﯶﯷﯸ
ﯹ
Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.
Verse 15
ﯺﯻﯼﯽ
ﯾ
Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?
Verse 16
ﯿﰀﰁﰂﰃﰄ
ﰅ
A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?
Verse 17
ﭑﭒﭓﭔﭕ
ﭖ
Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.
Verse 18
ﭗﭘﭙﭚﭛﭜ
ﭝ
"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.
Verse 19
ﭞﭟﭠﭡ
ﭢ
"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"
Verse 20
ﭣﭤﭥ
ﭦ
Sai ya nũna masa ãyar* nan mafi girma.
____________________
* Ãyar Mũsã da ta fi girma ita ce sandarsa mai zama maciji ko hannunsa mai haske kamar tõcila idan yã sanya cikin hammata yã fitar.
____________________
* Ãyar Mũsã da ta fi girma ita ce sandarsa mai zama maciji ko hannunsa mai haske kamar tõcila idan yã sanya cikin hammata yã fitar.
Verse 21
ﭧﭨ
ﭩ
Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
Verse 22
ﭪﭫﭬ
ﭭ
Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
Verse 23
ﭮﭯ
ﭰ
Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.
Verse 24
ﭱﭲﭳﭴ
ﭵ
Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."
Verse 25
ﭶﭷﭸﭹﭺ
ﭻ
Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
Verse 26
ﭼﭽﭾﭿﮀﮁ
ﮂ
Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.
Verse 27
Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.
Verse 28
ﮋﮌﮍ
ﮎ
Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.
Verse 29
ﮏﮐﮑﮒ
ﮓ
Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.
Verse 30
ﮔﮕﮖﮗ
ﮘ
Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.
Verse 31
ﮙﮚﮛﮜ
ﮝ
Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.
Verse 32
ﮞﮟ
ﮠ
Da duwatsu, Yã kafe ta.
Verse 33
ﮡﮢﮣ
ﮤ
Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.
Verse 34
ﮥﮦﮧﮨ
ﮩ
To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.
Verse 35
ﮪﮫﮬﮭﮮ
ﮯ
Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.
Verse 36
ﮰﮱﯓﯔ
ﯕ
Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.
Verse 37
ﯖﯗﯘ
ﯙ
To, amma wanda ya yi girman kai.
Verse 38
ﯚﯛﯜ
ﯝ
Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).
Verse 39
ﯞﯟﯠﯡ
ﯢ
To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.
Verse 40
Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.
Verse 41
ﯭﯮﯯﯰ
ﯱ
To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.
Verse 42
ﯲﯳﯴﯵﯶ
ﯷ
Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?
Verse 43
ﯸﯹﯺﯻ
ﯼ
Me ya haɗã ka da ambatonta?
Verse 44
ﯽﯾﯿ
ﰀ
Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.
Verse 45
ﰁﰂﰃﰄﰅ
ﰆ
Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.
Verse 46
Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.
تقدم القراءة