Fassarar Surar Nouh a الهوساوية daga الترجمة الهوساوية
Verse 1
Lalle ne Mun aiki Nũhu zuwa ga mutãnensa, cẽwa ka yi gargaɗi ga mutãnenka gabãnin wata azãba mai raɗaɗi ta zo musu.
Verse 2
ﮇﮈﮉﮊﮋﮌ
ﮍ
Ya ce: "Ya mutãnena ni, a gare ku, mai gargaɗi ne, mai bayyanãwa."
Verse 3
ﮎﮏﮐﮑﮒ
ﮓ
"Cewa ku bauta wa Allah, ku ji tsõronSa, kuma ku bĩ ni."
Verse 4
"Allah zai gãfarta muku daga zunubanku kuma Ya jinkirta muku zuwa ga ajalin da aka ambata. Lalle ne ajalin Allah idan ya zo, ba za a jinkirta Shi ba, dã kun kasance masana (ga abin da nake faɗã dã, kun bar kãfirci)."
Verse 5
Nũhu) ya ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne, na kirãyi mutãnena, a cikin dare da yini."
Verse 6
ﮱﯓﯔﯕﯖ
ﯗ
"To, amma kirana bai ƙãre su ba sai da, gudu (daga gare ni)."
Verse 7
"Kuma lalle ne ni, kõ da yaushe na kirãye su dõmin Ka gãfarta musu, sai su sanya yatsunsu a cikin kunnuwansu, su lulluɓe da tufãfinsu, su dõge ga yin laifi. Sun yi girman kai iyãkar girman kai."
Verse 8
ﯧﯨﯩﯪ
ﯫ
"Sa'an nan lalle ne ni, na kira su, a bayyane."
Verse 9
"Sa'an nan lalle ne, na yi yẽkuwa sabõda su, kuma na gãna da su a cikin asĩri."
Verse 10
ﯴﯵﯶﯷﯸﯹ
ﯺ
"Shi na ce, 'Ku nẽmi gãfara daga Ubangijinku, lalle ne shi Ya kasance Mai gãfara ne."
Verse 11
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
"Ya sako (girgijen) sama a kanku da ruwa mai ɓuɓɓuga."
Verse 12
"Kuma ya yalwata muku game da dũkiya da ɗiya, Ya sanya muku (albarka) ga gõnaki, kuma Ya sanya muku koguna."
Verse 13
ﭠﭡﭢﭣﭤﭥ
ﭦ
"Me ya sãme ku, bã ku fãtar sãmun natsuwa daga Allah,"
Verse 14
ﭧﭨﭩ
ﭪ
"Alhãli kuwa, lalle ne, Ya halitta. ku, a cikin hãlãye?"
Verse 15
"Ba ku ga yadda Allah Ya halitta wasu sammai bakwai ɗabaƙõƙĩ a kan jũna ba?"
Verse 16
"Ya sanya watã a cikinsu, yana mai haske, Ya sanya rãnã babbar fitila?"
Verse 17
ﭼﭽﭾﭿﮀ
ﮁ
"Kuma Allah Ya tsirar da ku daga ƙasa (kamar ganye) tsirarwa."
Verse 18
ﮂﮃﮄﮅﮆ
ﮇ
"Sa'an nan Ya mayar da ku a cikinta, kuma Ya fitar da ku fitarwa."
Verse 19
ﮈﮉﮊﮋﮌ
ﮍ
"Kuma Allah Ya sanya muku ƙasa shimfidaɗɗiya."
Verse 20
ﮎﮏﮐﮑ
ﮒ
"Dõmin ku shiga a cikinta, hanyõyi mãsu fãɗi."
Verse 21
Nũhu ya ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne sũ sun saɓa mini sun bi wanda dukiyarsa da ɗiyansa ba su ƙãre shi da kõme ba sai da hasãra."
Verse 22
ﮡﮢﮣ
ﮤ
"Kuma sun yi wani mãkirci, mãkirci babba."
Verse 23
"Kuma suka ce: Faufau kada ku bar gumãkanku, kuma faufau, kada ku bar wadda, kuma kada ku bar suwã kuma kada ku bar Yagũsa da Ya'ũƙa da Nasra."
Verse 24
"Kuma lalle ne sun ɓatar da (mutãne) mãsu yawa, kuma kada Ka ƙãrã wa azzãlumai (kõme) sai ɓata."
Verse 25
Sabõda laifukansu na ganganci aka nutsar da su, sa'an nan aka sanya su a wuta. Saboda haka ba su sãmã wa kansu wani mataimaki wanin Allah ba.
Verse 26
Kuma Nũhu ya ce: "Ya Ublngijina! Kada Ka bari, a kan ƙasa, daga cikin kãfirai, wanda ke zama a cikin gida."
Verse 27
"Lalle ne, Kai idan Ka bar su, zã su ɓatar da bãyinKa, kuma bã zã su haifi kowa ba fãce fãjiri mai yawan kãfirci"
Verse 28
"Ya Ubanginjina! Ka yi mini gãfara (ni) da mahaifana biyu, da wanda ya shiga gidana, yana mai ĩmãni, da mũminai maza da mũminai mãtã, kuma kada Ka ƙãrã wa azzãlumai kõme sai halaka."
تقدم القراءة