Fassarar Surar Al'Alak a الهوساوية daga الترجمة الهوساوية
Verse 1
ﮕﮖﮗﮘﮙ
ﮚ
Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta.
Verse 2
ﮛﮜﮝﮞ
ﮟ
Ya hahitta mutum daga gudan jini.
Verse 3
ﮠﮡﮢ
ﮣ
Ka yi karatu, kuma UbangiJinka shi ne Mafi karimci.
Verse 4
ﮤﮥﮦ
ﮧ
Wanda Ya sanar (da mutum) game da alƙalami.
Verse 5
ﮨﮩﮪﮫﮬ
ﮭ
Ya sanar da mutum abin da bai sani ba.
Verse 6
ﮮﮯﮰﮱ
ﯓ
A'aha! Lalle, ne mutum haƙĩƙa, yana girman kai (ya ƙi karatu).
Verse 7
ﯔﯕﯖ
ﯗ
Dõmin yã ga kansa, yã wadãta.
Verse 8
ﯘﯙﯚﯛ
ﯜ
Lalle ne zuwa ga Ubangijinka makoma take.
Verse 9
ﯝﯞﯟ
ﯠ
Shin, kã ga wanda ke hana.
Verse 10
ﯡﯢﯣ
ﯤ
Bãwã idan yã yi salla?
Verse 11
ﯥﯦﯧﯨﯩ
ﯪ
Ashe, kã gani, idan (shi bãwan) ya kasance a kan shiriya?
Verse 12
ﯫﯬﯭ
ﯮ
Ko ya yi umurni da taƙawa?
Verse 13
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
Ashe, kã gani, idan (shi mai hanin) ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya?
Verse 14
ﭖﭗﭘﭙﭚ
ﭛ
Ashe, bai sani ba cewa Allah Yanã gani?
Verse 15
ﭜﭝﭞﭟﭠﭡ
ﭢ
A'aha! Lalle ne, idan bai hanu ba, lalle ne zã Mu ja gãshin makwarkwaɗa.
Verse 16
ﭣﭤﭥ
ﭦ
Makwarkwaɗa maƙaryaciya, mai laifi.
Verse 17
ﭧﭨ
ﭩ
Sai ya kirayi ƙungiyarsa.
Verse 18
ﭪﭫ
ﭬ
Zã Mu kirayi zabaniyãwa (mala'iku mãsu girma).
Verse 19
ﭭﭮﭯﭰﭱﭲ
ﭳ
A'aha kada ka bĩ shi. Kuma ka yi tawali'u,* kuma ka nemi kusanta (zuwa ga Ubangijinka).
____________________
* Wato salla da sauran ibãdu.
____________________
* Wato salla da sauran ibãdu.
تقدم القراءة