Fassarar Surar An-Takwir a الهوساوية daga الترجمة الهوساوية
Verse 1
ﭙﭚﭛ
ﭜ
Idan rãna aka shafe haskenta
Verse 2
ﭝﭞﭟ
ﭠ
Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).
Verse 3
ﭡﭢﭣ
ﭤ
Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.
Verse 4
ﭥﭦﭧ
ﭨ
Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna* aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.
____________________
* Rãƙuma mãsu ciki ɗan wata gõma.
____________________
* Rãƙuma mãsu ciki ɗan wata gõma.
Verse 5
ﭩﭪﭫ
ﭬ
Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.
Verse 6
ﭭﭮﭯ
ﭰ
Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.
Verse 7
ﭱﭲﭳ
ﭴ
Kuma idan rãyuka aka haɗa* su da jikunkunansu.
____________________
* Ko kuma, aka haɗa kõwane mutum da irin mutãnensa a Aljanna ko a wuta.
____________________
* Ko kuma, aka haɗa kõwane mutum da irin mutãnensa a Aljanna ko a wuta.
Verse 8
ﭵﭶﭷ
ﭸ
Kuma idan wadda aka turbuɗe* ta da rai aka tambaye ta.
____________________
* A cikin zãmanin jahiliyya Lãrabãwa bã su son a haifa musu 'ya'ya mãta dõmin haka har sukan turbuɗe 'ya'yansu dõmin kada su yi abin kunya ko kuma su talauce wajen yi musu aure.
____________________
* A cikin zãmanin jahiliyya Lãrabãwa bã su son a haifa musu 'ya'ya mãta dõmin haka har sukan turbuɗe 'ya'yansu dõmin kada su yi abin kunya ko kuma su talauce wajen yi musu aure.
Verse 9
ﭹﭺﭻ
ﭼ
"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"
Verse 10
ﭽﭾﭿ
ﮀ
Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).
Verse 11
ﮁﮂﮃ
ﮄ
Kuma idan sama aka fẽɗe ta.
Verse 12
ﮅﮆﮇ
ﮈ
Kuma idan Jahĩm aka hũra ta
Verse 13
ﮉﮊﮋ
ﮌ
Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.
Verse 14
ﮍﮎﮏﮐ
ﮑ
Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).
Verse 15
ﮒﮓﮔ
ﮕ
To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã* ba.
____________________
* Masu tafiya suna kõmawa bãya.
____________________
* Masu tafiya suna kõmawa bãya.
Verse 16
ﮖﮗ
ﮘ
Mãsu gudu suna ɓũya.
Verse 17
ﮙﮚﮛ
ﮜ
Da dare idan ya bãyar da bãya.
Verse 18
ﮝﮞﮟ
ﮠ
Da sãfiya idan ta yi lumfashi.
Verse 19
ﮡﮢﮣﮤ
ﮥ
Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.
Verse 20
ﮦﮧﮨﮩﮪﮫ
ﮬ
Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.
Verse 21
ﮭﮮﮯ
ﮰ
Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.
Verse 22
ﮱﯓﯔ
ﯕ
Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.
Verse 23
ﯖﯗﯘﯙ
ﯚ
Kuma lalle ne, yã gan shi(5) a cikin sararin sama mabayyani.
____________________
(5) Annabi ya ga Mala'ika Jibirilu ya san shi. Sabõda haka wani aljani bã zai yi kama da shi ba balle ya kãwo masa ƙarya.
____________________
(5) Annabi ya ga Mala'ika Jibirilu ya san shi. Sabõda haka wani aljani bã zai yi kama da shi ba balle ya kãwo masa ƙarya.
Verse 24
ﯛﯜﯝﯞﯟ
ﯠ
Kuma shi, ga gaibi(6) bã mai rowa ba ne.
____________________
(6) Ma'anar gaibi a nan, ilmin da Allah Ya aiko Jibirilu da shi zuwa ga Annabi Annabi ba ya ɓõye shi daga mutãne. Ga wata ƙira'a, wanda ake tuhuma, wãto ba a tuhumar Annabi, ga gaibin da ya faɗi cewa daga Allah yake, wato Alƙur'ãni duka gaskiya ne.
____________________
(6) Ma'anar gaibi a nan, ilmin da Allah Ya aiko Jibirilu da shi zuwa ga Annabi Annabi ba ya ɓõye shi daga mutãne. Ga wata ƙira'a, wanda ake tuhuma, wãto ba a tuhumar Annabi, ga gaibin da ya faɗi cewa daga Allah yake, wato Alƙur'ãni duka gaskiya ne.
Verse 25
ﯡﯢﯣﯤﯥ
ﯦ
Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.
Verse 26
ﯧﯨ
ﯩ
Shin, a inã zã ku tafi?
Verse 27
ﯪﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.
Verse 28
ﯰﯱﯲﯳﯴ
ﯵ
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.
Verse 29
Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.
تقدم القراءة