Fassarar Surar An-Takwir a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
Verse 1
ﭙﭚﭛ
ﭜ
An-Takwir
Idan rãna aka shafe haskenta
Verse 2
ﭝﭞﭟ
ﭠ
Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).
Verse 3
ﭡﭢﭣ
ﭤ
Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.
Verse 4
ﭥﭦﭧ
ﭨ
Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.
Verse 5
ﭩﭪﭫ
ﭬ
Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.
Verse 6
ﭭﭮﭯ
ﭰ
Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.
Verse 7
ﭱﭲﭳ
ﭴ
Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.
Verse 8
ﭵﭶﭷ
ﭸ
Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.
Verse 9
ﭹﭺﭻ
ﭼ
"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"
Verse 10
ﭽﭾﭿ
ﮀ
Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).
Verse 11
ﮁﮂﮃ
ﮄ
Kuma idan sama aka fẽɗe ta.
Verse 12
ﮅﮆﮇ
ﮈ
Kuma idan Jahĩm aka hũra ta
Verse 13
ﮉﮊﮋ
ﮌ
Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.
Verse 14
ﮍﮎﮏﮐ
ﮑ
Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).
Verse 15
ﮒﮓﮔ
ﮕ
To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.
Verse 16
ﮖﮗ
ﮘ
Mãsu gudu suna ɓũya.
Verse 17
ﮙﮚﮛ
ﮜ
Da dare idan ya bãyar da bãya.
Verse 18
ﮝﮞﮟ
ﮠ
Da sãfiya idan ta yi lumfashi.
Verse 19
ﮡﮢﮣﮤ
ﮥ
Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.
Verse 20
ﮦﮧﮨﮩﮪﮫ
ﮬ
Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.
Verse 21
ﮭﮮﮯ
ﮰ
Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.
Verse 22
ﮱﯓﯔ
ﯕ
Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.
Verse 23
ﯖﯗﯘﯙ
ﯚ
Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani.
Verse 24
ﯛﯜﯝﯞﯟ
ﯠ
Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne.
Verse 25
ﯡﯢﯣﯤﯥ
ﯦ
Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.
Verse 26
ﯧﯨ
ﯩ
Shin, a inã zã ku tafi?
Verse 27
ﯪﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.
Verse 28
ﯰﯱﯲﯳﯴ
ﯵ
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.
Verse 29
Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.
تقدم القراءة