Fassarar Surar Al-Ma'arij a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
Verse 1
ﮮﮯﮰﮱ
ﯓ
Al-Ma'arij
Wani mai tambaya yã yi tambaya game da azãba, mai aukuwa.
Verse 2
ﯔﯕﯖﯗ
ﯘ
Ga kãfirai, bã ta da mai tunkuɗẽwa.
Verse 3
ﯙﯚﯛﯜ
ﯝ
Daga Allah Mai matãkala.
Verse 4
Malã'iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne.
Verse 5
ﯪﯫﯬ
ﯭ
Sabõda haka, ka yi haƙuri, haƙuri mai kyãwo.
Verse 6
ﯮﯯﯰ
ﯱ
Lalle ne su, sunã ganin ta mai nĩsa.
Verse 7
ﯲﯳ
ﯴ
Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa.
Verse 8
ﯵﯶﯷﯸ
ﯹ
Rãnar da sama zã ta kasance kamar narkakkar azurfa.
Verse 9
ﯺﯻﯼ
ﯽ
Kuma duwãtsu su zama kamar saɓin sũfi.
Verse 10
ﯾﯿﰀﰁ
ﰂ
Kuma abõki bã ya tambayar inda wani abõki yake.
Verse 11
Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa,
Verse 12
ﭜﭝ
ﭞ
Da matarsa da ɗan'uwansa.
Verse 13
ﭟﭠﭡ
ﭢ
Da danginsa, mãsu tattarã shi.
Verse 14
ﭣﭤﭥﭦﭧﭨ
ﭩ
Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsĩrar da shi.
Verse 15
ﭪﭫﭬﭭ
ﭮ
A'aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã,
Verse 16
ﭯﭰ
ﭱ
Mai twãle fãtar goshi.
Verse 17
ﭲﭳﭴﭵ
ﭶ
Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.
Verse 18
ﭷﭸ
ﭹ
Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka.
Verse 19
ﭺﭻﭼﭽﭾ
ﭿ
Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi.
Verse 20
ﮀﮁﮂﮃ
ﮄ
Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri.
Verse 21
ﮅﮆﮇﮈ
ﮉ
Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa.
Verse 22
ﮊﮋ
ﮌ
Sai mãsu yin salla,
Verse 23
ﮍﮎﮏﮐﮑ
ﮒ
Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.
Verse 24
ﮓﮔﮕﮖﮗ
ﮘ
Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.
Verse 25
ﮙﮚ
ﮛ
Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon.
Verse 26
ﮜﮝﮞﮟ
ﮠ
Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako.
Verse 27
ﮡﮢﮣﮤﮥﮦ
ﮧ
Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.
Verse 28
ﮨﮩﮪﮫﮬ
ﮭ
Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.
Verse 29
ﮮﮯﮰﮱ
ﯓ
Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne.
Verse 30
Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.
Verse 31
To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka.
Verse 32
ﯧﯨﯩﯪﯫ
ﯬ
Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.
Verse 33
ﯭﯮﯯﯰ
ﯱ
Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.
Verse 34
ﯲﯳﯴﯵﯶ
ﯷ
Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.
Verse 35
ﯸﯹﯺﯻ
ﯼ
Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne
Verse 36
ﯽﯾﯿﰀﰁ
ﰂ
Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu).
Verse 37
ﰃﰄﰅﰆﰇ
ﰈ
Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama'a-jama'a!
Verse 38
Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni'ima ne (ba da wani aiki ba)?
Verse 39
ﰒﰓﰔﰕﰖﰗ
ﰘ
A'aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani.
Verse 40
Sabõda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wurãren ɓullõwar rãna da wurãren fãɗuwarta ba, lalle Mũ, Mãsu iyãwa ne.
Verse 41
Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alhẽri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda ake rinjãya ba.
Verse 42
Sabõda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wãsã, har su haɗu da rãnarsu wadda ake yi musu alkawari (da ita).
Verse 43
Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata kafaffiyar (tuta), suke yin gaugãwa.
Verse 44
Maƙaskanta ga idanunsu, wani walakanci yana rufe su. wannan shi ne yinin da suka kasance ana yi musa alkawari (a kansa.)
تقدم القراءة