Fassarar Surar Al-Muddasir a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
Verse 1
ﮪﮫ
ﮬ
Al-Muddasir
Yã wanda ya lulluɓa da mayãfi.
Verse 2
ﮭﮮ
ﮯ
Ka tãshi dõmin ka yi gargaɗi
Verse 3
ﮰﮱ
ﯓ
Kuma Ubangijinka, sai ka girmama Shi,
Verse 4
ﯔﯕ
ﯖ
Kuma tutãfinka, sai ka tsarkake su,
Verse 5
ﯗﯘ
ﯙ
Kuma gumãka, sai ka ƙaurace musu.
Verse 6
ﯚﯛﯜ
ﯝ
Kada ka yi kyauta kana nẽman ƙãri
Verse 7
ﯞﯟ
ﯠ
Kuma sabõda Ubangijinka? Sai ka yi haƙure
Verse 8
ﯡﯢﯣﯤ
ﯥ
To, idan aka yi bũsa a cikin ƙaho.
Verse 9
ﯦﯧﯨﯩ
ﯪ
To, wannan, a rãnar nan, yini ne mai wuya
Verse 10
ﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
A kan kãfirai, bã mai sauƙi ba ne.
Verse 11
ﯰﯱﯲﯳ
ﯴ
Ka bar Ni da wanda Na halitta, yana shi kaɗai,
Verse 12
ﯵﯶﯷﯸ
ﯹ
Kuma Na sanya masa dũkiya shimfiɗaɗɗiya
Verse 13
ﯺﯻ
ﯼ
Da ɗiyã halartattu,
Verse 14
ﯽﯾﯿ
ﰀ
Kuma Na shimfiɗa? masa kõme shimfiɗãwa.
Verse 15
ﰁﰂﰃﰄ
ﰅ
Sa'an nan, yanã kwaɗayin in yi masa ƙãri!
Verse 16
ﰆﰇﰈﰉﰊﰋ
ﰌ
Faufau! Lalle ne, shĩ yã kasance, ga ãyõyinMu, mai tsaurin kai.
Verse 17
ﰍﰎ
ﰏ
Zã Ni kallafa masa wahala mai hauhawa.
Verse 18
ﰐﰑﰒ
ﰓ
Lalle ne, Shi, yã yi tunãni, kuma yã ƙaddara (abin da zai faɗã game da Alƙur'ãni)
Verse 19
ﭑﭒﭓ
ﭔ
Sabõda haka, aka la'ane shi, kamar yadda ya ƙaddara.
Verse 20
ﭕﭖﭗﭘ
ﭙ
Sa'an nan, aka la'ane shi kamar yadda ya ƙaddara.
Verse 21
ﭚﭛ
ﭜ
Sa'an nan, ya yi tunãni
Verse 22
ﭝﭞﭟ
ﭠ
Sa'an nan, ya gintse huska? kuma ya yi murtuk.
Verse 23
ﭡﭢﭣ
ﭤ
Sa'an nan, ya jũya bãya, kuma ya bunƙãsa,
Verse 24
ﭥﭦﭧﭨﭩﭪ
ﭫ
Sai ya ce: "Wannan abu dai bã kõme ba ne fãce wani sihiri, wanda aka ruwaito."
Verse 25
ﭬﭭﭮﭯﭰ
ﭱ
"Wannan maganar mutum dai ce."
Verse 26
ﭲﭳ
ﭴ
Zã Ni ƙõna shi da Saƙar.
Verse 27
ﭵﭶﭷﭸ
ﭹ
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽwa Saƙar!
Verse 28
ﭺﭻﭼﭽ
ﭾ
Bã ta ragẽwa, kuma bã ta bari.
Verse 29
ﭿﮀ
ﮁ
Mai nãcẽwa ga jiki ce (da (ƙũna).
Verse 30
ﮂﮃﮄ
ﮅ
A kanta akwai (matsara) gõma shã tara.
Kuma ba Mu sanya ma'abũta wutã (wãto matsaranta) ba, fãce malã'iku, kuma ba Mu sanya adadinsu (gõma sha tara) ba, fãce dõmin fitina ga waɗanda suka kãfirta domin waɗanda aka bai wa littãfi su sãmi yaƙĩni kuma waɗanda suka yi ĩmãni su ƙãra ĩmãni, kuma waɗanda aka bai wa littãfi da mũminai bã zã su yi shakka ba, kuma domin wa ɗanda a cikin zukatansu akwai wata cuta da kãfirai su ce: "Mẽ Allah Yake nufi da wannan, ya kasance misãli?" Haka dai Allah ke ɓatar da wanda Ya so, kuma Ya shiryar da wanda ya so. Kuma bãbu wanda ya san mayãƙan Ubangijinka fãce Shi, kuma ita (wutar) ba ta kasance ba fãce wata tunãtarwa ce ga mutum.
Verse 32
ﯥﯦ
ﯧ
A'aha! Ina rantsuwa da watã.
Verse 33
ﯨﯩﯪ
ﯫ
Da dare a lõkacin da ya jũyar da baya.
Verse 34
ﯬﯭﯮ
ﯯ
Da sãfiya idan ta wãye.
Verse 35
ﯰﯱﯲ
ﯳ
Ita (wutar) ɗayan manyan masĩfũ? ce.
Verse 36
ﯴﯵ
ﯶ
Mai gargaɗĩ ce ga mutum.
Verse 37
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya gabãta ko ya jinkirta.
Verse 38
ﯿﰀﰁﰂﰃ
ﰄ
Kõwane rai ga abin da ya aikata jingina ce.
Verse 39
ﰅﰆﰇ
ﰈ
Fãce mutãnen dãma.
Verse 40
ﰉﰊﰋ
ﰌ
A cikin Aljanna suna tambayar jũna.
Verse 41
ﰍﰎ
ﰏ
Game da mãsu laifi.
Verse 42
ﰐﰑﰒﰓ
ﰔ
(Su ce musu) "Me ya shigar da ku a cikin Saƙar?"
Verse 43
ﰕﰖﰗﰘﰙ
ﰚ
Suka ce: "Ba mu kasance munã a cikin mãsu salla ba."
Verse 44
ﰛﰜﰝﰞ
ﰟ
"Kuma ba mu kasance muna ciyar da matalautã ba."
Verse 45
ﰠﰡﰢﰣ
ﰤ
"Kuma mun kasance muna kũtsãwa tãre da mãsu kũtsãwa."
Verse 46
ﰥﰦﰧﰨ
ﰩ
"Mun kasance munã ƙaryata rãnar sãkamako."
Verse 47
ﰪﰫﰬ
ﰭ
"Har gaskiya (wãto mutuwa) ta zo mana."
Verse 48
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
Sabõda haka cẽton mãsu cẽto bã zai amfãne su ba.
Verse 49
ﭖﭗﭘﭙﭚ
ﭛ
Haba! Me ya same su, suka zama mãsu bijirewa daga wa'azin gaskiya.
Verse 50
ﭜﭝﭞ
ﭟ
Kamar dai sũ, jãkuna firgitattu ne.
Verse 51
ﭠﭡﭢ
ﭣ
Sun gudu daga zãki.
Verse 52
A'aha! Kõwãne mutum daga cikinsu yanã son a zo masa da takardu (da sũnansa) ana wãtsãwa
Verse 53
ﭮﭯﭰﭱﭲﭳ
ﭴ
A'aha! Kai dai, bã su jin tsõron Lãhira.
Verse 54
ﭵﭶﭷ
ﭸ
A'aha! Lalle ne, shi (Alƙur'ãni) tunãtarwa ce.
Verse 55
ﭹﭺﭻ
ﭼ
Dõmin wanda ya so, ya tuna.
Verse 56
Kuma bã zã su tuna ba fãce idan Allah Ya so, Shi ne Ya cancanta a bi Shi da taƙawa kuma Ya cancanta ga Ya yi gãfara.
تقدم القراءة