Fassarar Surar Al-Lail a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
Verse 1
ﮡﮢﮣ
ﮤ
Al-Lail
Inã rantsuwa da dare a lõkacin da yake rufẽwa.
Verse 2
ﮥﮦﮧ
ﮨ
Da yini a lõkacin da yake kuranyẽwa.
Verse 3
ﮩﮪﮫﮬ
ﮭ
Da abin da ya halitta namiji da mace.
Verse 4
ﮮﮯﮰ
ﮱ
Lãlle ne ayyukanku, dabam-dabam suke.
Verse 5
ﯓﯔﯕﯖ
ﯗ
To, amma wanda ya yi kyauta, kuma ya yi taƙawa.
Verse 6
ﯘﯙ
ﯚ
Kuma ya gaskata kalma mai kyãwo.
Verse 7
ﯛﯜ
ﯝ
To, zã Mu sauƙaƙe masa har ya kai ga sauƙi.
Verse 8
ﯞﯟﯠﯡ
ﯢ
Kuma amma wanda ya yi rõwa, kuma ya wadãtu da kansa.
Verse 9
ﯣﯤ
ﯥ
Kuma ya ƙaryatar da kalma mai kyãwo.
Verse 10
ﭑﭒ
ﭓ
To, zã Mu sauƙaƙke masa har ya kai ga tsanani.
Verse 11
ﭔﭕﭖﭗﭘﭙ
ﭚ
Kuma dũkiyarsa ba ta wadãtar masa da kõme ba, a lõkacin da ya gangara (a wuta).
Verse 12
ﭛﭜﭝ
ﭞ
Lãlle aikinMu ne, Mu bayyana shiriya.
Verse 13
ﭟﭠﭡﭢ
ﭣ
Kuma lalle ne Lãhira da duniya Namu ne.
Verse 14
ﭤﭥﭦ
ﭧ
Sabõda haka, Na yi maku gargaɗi da wuta mai babbaka.
Verse 15
ﭨﭩﭪﭫ
ﭬ
Bãbu mai shigarta sai mafi shaƙãwa.
Verse 16
ﭭﭮﭯ
ﭰ
Wanda ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya.
Verse 17
ﭱﭲ
ﭳ
Kuma mafi taƙawa zai nisance ta.
Verse 18
ﭴﭵﭶﭷ
ﭸ
Wanda yake bãyar da dũkiyarsa, alhãli yana tsarkaka.
Verse 19
ﭹﭺﭻﭼﭽﭾ
ﭿ
Alhãli bãbu wani mai wata ni'ima wurinsa wadda ake nẽman sakamakonta.
Verse 20
ﮀﮁﮂﮃﮄ
ﮅ
Fãce dai nẽman yardar Ubangijinsa Mafi ɗaukaka.
Verse 21
ﮆﮇ
ﮈ
To, lalle ne zai yarda (da sakamakon da zã a bã shi).
تقدم القراءة