Fassarar Surar At-Tarik a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
Verse 1
ﭑﭒ
ﭓ
At-Tarik
Inã rantsuwa da sama da mai aukõwa da dare.
Verse 2
ﭔﭕﭖﭗ
ﭘ
To, mẽ yã sanar da kai abin da ake cẽwa mai aukõwa da dare?
Verse 3
ﭙﭚ
ﭛ
Shi ne taurãron nan mai tsananin haske.
Verse 4
ﭜﭝﭞﭟﭠﭡ
ﭢ
Bãbu wani rai fãce a kansa akwai wani mai tsaro.
Verse 5
ﭣﭤﭥﭦ
ﭧ
To, mutum ya dũba, daga mẽ aka halittã shi?
Verse 6
ﭨﭩﭪﭫ
ﭬ
An halittã shi daga wani ruwa mai tunkuɗar jũna.
Verse 7
ﭭﭮﭯﭰﭱ
ﭲ
Yanã fita daga tsakanin tsatso da karankarman ƙirji.
Verse 8
ﭳﭴﭵﭶ
ﭷ
Lalle ne Shi (Allah), ga mayar da shi (mutum), tabbas Mai iyãwa ne.
Verse 9
ﭸﭹﭺ
ﭻ
Rãnar da ake jarrabawar asirai.
Verse 10
ﭼﭽﭾﭿﮀﮁ
ﮂ
Saboda haka, bã shi da wani ƙarfi, kuma bã shi da wani mai taimako (da zai iya kãre shi daga azãbar Allah).
Verse 11
ﮃﮄﮅ
ﮆ
Ina rantsuwa da sama ma'abũciyar ruwa mai kõmãwa yana yankẽwa.
Verse 12
ﮇﮈﮉ
ﮊ
Da ƙasa ma'abũciyar tsãgẽwa,
Verse 13
ﮋﮌﮍ
ﮎ
Lalle ne shĩ (Alƙur'ãni), haƙĩƙa magana ce daki-daki
Verse 14
ﮏﮐﮑ
ﮒ
Kuma shĩ bã bananci bane
Verse 15
ﮓﮔﮕ
ﮖ
Lalle ne sũ, suna ƙulla kaidi na sõsai.
Verse 16
ﮗﮘ
ﮙ
Kuma Ni, Ina mayar da kaidi (gare su) kamar yadda suke ƙulla kaidi.
Verse 17
ﮚﮛﮜﮝ
ﮞ
Saboda haka, ka yi wa kafirai jinkiri, ka dakata musu, sannu-sannu.
تقدم القراءة