Fassarar Surar Az-Zariyat a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
Verse 1
ﯤﯥ
ﯦ
Az-Zariyat
Inã rantsuwa da iskõki mãsu shẽkar abũbuwa, shẽƙẽwa.
Verse 2
ﯧﯨ
ﯩ
Sa'an nan da girãgizai mãsu ɗaukar nauyi (na ruwa).
Verse 3
ﯪﯫ
ﯬ
Sa'an nan da jirãge mãsu gudãna (a kan ruwa) da sauƙi.
Verse 4
ﯭﯮ
ﯯ
Sa'an nan da Malã'iku mãsu rabon al'amari (bisa umurnin Allah).
Verse 5
ﯰﯱﯲ
ﯳ
Lalle abin da ake yi muku alkawari (da zuwansa), haƙĩƙa gaskiya ne.
Verse 6
ﯴﯵﯶ
ﯷ
Kuma lalle sakamako (ga ayyukanku), haƙĩƙa, mai aukuwa ne
Verse 7
ﭑﭒﭓ
ﭔ
Inã rantsuwa da samã ma'abũciyar hanyõyi (na tafiyar taurãri da sautin rediyo).
Verse 8
ﭕﭖﭗﭘ
ﭙ
Lalle kũ, haƙĩƙa, kunã cikin magana mai sãɓa wa juna (game da Alƙur'ani).
Verse 9
ﭚﭛﭜﭝ
ﭞ
Anã karkatar da wanda aka jũyar (daga gaskiya).
Verse 10
ﭟﭠ
ﭡ
An la'ani mãsu ƙiri-faɗi.
Verse 11
ﭢﭣﭤﭥﭦ
ﭧ
Waɗanda suke shagala a cikin zurfin jãhilci.
Verse 12
ﭨﭩﭪﭫ
ﭬ
Sunã tambaya: "Yaushe ne rãnar sakamako zã ta auku?"
Verse 13
ﭭﭮﭯﭰﭱ
ﭲ
Ranar da suke a kan wuta anã fitinar su.
Verse 14
(A ce musu): "Ku ɗanɗani fitinarku, wannan shĩ ne abin da kuka kasance kunã nẽman zuwansa da gaggãwa."
Verse 15
ﭻﭼﭽﭾﭿ
ﮀ
Lalle mãsu taƙawa, sunã a cikin lambunan itãce da marẽmari.
Verse 16
Sunã mãsu dĩbar abin da Ubangijinsu Ya bã su. Lalle sũ, sun kasance mãsu kyautatãwa a gabãnin haka (a dũniya).
Verse 17
ﮌﮍﮎﮏﮐﮑ
ﮒ
Sun kasance a lõkaci kaɗan na dare suke yin barci.
Verse 18
ﮓﮔﮕ
ﮖ
Kuma a lõkutan asuba sunã ta yin istigfãri.
Verse 19
ﮗﮘﮙﮚﮛ
ﮜ
Kuma a cikin dũkiyarsu akwai hakki ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hana wa rõƙo.
Verse 20
ﮝﮞﮟﮠ
ﮡ
Kuma a cikin ƙasã akwai ãyõyi ga mãsu yaƙĩni.
Verse 21
ﮢﮣﮤﮥﮦ
ﮧ
Kuma a cikin rãyukanku (akwai ãyõyi). To, bã zã ku dũbã ba?
Verse 22
ﮨﮩﮪﮫﮬ
ﮭ
Kuma a cikin sama arzikinku (yake fitõwa) da abin da ake yi muku alkawari.
Verse 23
To, kuma Ina rantsuwa da Ubangijin sama da ƙasã, lalle shĩ (abin da ake yi muku alkawari), haƙĩƙa gaskiya ne, kamar abin da kuka zamo kunã karantãwa na magana,
Verse 24
ﯙﯚﯛﯜﯝﯞ
ﯟ
Shin, lãbãrin Bãƙin Ibrãhĩm, waɗanda aka girmama, ya zo maka?
Verse 25
A lõkacin da suka shiga gare shi, sai suka yi sallama; ya ce "Aminci ya tabbata a gare ku, mutãne bãƙi!"
Verse 26
ﯫﯬﯭﯮﯯﯰ
ﯱ
Sai ya jũya zuwa ga iyãlinsa, sa'an nan ya zo da maraƙi tutturna,
Verse 27
ﯲﯳﯴﯵﯶ
ﯷ
Sai ya kusantar da shi zuwa gare su, ya ce: "Bã zã ku ci ba?"
Verse 28
Sai ya ji tsõro daga gare su. Suka ce: "Kada kaji tsõro." Kuma suka yi masa bushãra da (haihuwar) wani yaro mai ilmi.
Verse 29
Sai matarsa ta fuskanta cikin ƙyallõwa, har ta mari fuskarta kuma ta ce: "Tsõhuwa bakarãriya (zã ta haihu)!"
Verse 30
Suka ce: "Kamar haka Ubangijinki Ya faɗa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai hikima, Mai ilmi."
Verse 31
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
(Ibrãĩm) ya ce: "To mẽne ne babban al'almarinku, yã kũ Manzanni!"
Verse 32
ﭘﭙﭚﭛﭜﭝ
ﭞ
Suka ce: "Lalle mũ, an aike mu zuwa ga waɗansu mutãne, mãsu laifi.
Verse 33
ﭟﭠﭡﭢﭣ
ﭤ
"Dõmin mu saka musu waɗansu duwãtsu na wani yumɓu (bom).
Verse 34
ﭥﭦﭧﭨ
ﭩ
"Waɗanda aka yi wa alãma daga wajen Ubangijinka, dõmin mãsu ɓarna."
Verse 35
ﭪﭫﭬﭭﭮﭯ
ﭰ
Sa'an, nan Muka fitar da wanda ya kasance a cikinta daga mũminai.
Verse 36
Sai dai ba mu sãmu ba, a cikinta, fãce gida guda na Musulmi.
Verse 37
Kuma Muka bar wata ãyã, a cikinta, ga waɗanda ke jin tsõron azãba, mai raɗaɗi.
Verse 38
Kuma ga Mũsã, a lõkacin da Muka aiko shi zuwa ga Fir'auna da wani dalĩli bayyananne.
Verse 39
ﮊﮋﮌﮍﮎﮏ
ﮐ
Sai ya jũya bãya tãre da ƙarfinsa, kuma ya ce: "Mai sihiri ne kõ kuwa mahaukaci!"
Verse 40
Sabõda haka, Muka kama shi tãre da rundunarsa, sa'an nan Muka jẽfa su a cikin tẽku, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
Verse 41
Kuma ga Ãdãwa, a lõkacin da Muka aika iska ƙẽƙasasshiya a kansu.
Verse 42
Bã ta barin kõme da ta jẽ a kansa, fãce ta mayar da shi kamar rududdugaggun ƙasũsuwa.
Verse 43
Kuma ga Samũdãwa, a lõkacin da aka ce musu: "Ku ji ɗan dãɗi har wani ɗan lõkaci,"
Verse 44
Sai suka yi girman kai ga umurnin Ubangijinsu, sabõda haka tsãwa ta kãma su, alhãli kuwa sunã kallo.
Verse 45
Ba su kõ sãmu dãmar tsayãwa ba, kuma ba su kasance mãsu nẽman ãgaji ba.
Verse 46
Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sun kasance waɗansu irin mutãne ne fãsiƙai.
Verse 47
ﯰﯱﯲﯳﯴ
ﯵ
Kuma sama, mun gina ta da wani irin ƙarfi, alhãli kuwa lalle Mũ ne Mãsu yalwatãwa.
Verse 48
ﯶﯷﯸﯹ
ﯺ
Kuma ƙasã Mun shimfiɗa ta, To, madalla da mãsu shimfiɗãwa, Mũ,
Verse 49
Kuma daga kõme Mun halitta nau'i biyu, watakila zã ku yi tunãni.
Verse 50
Sabõda haka ku gudu zuwa ga Allah, lalle nĩ mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.
Verse 51
Kuma kada ku sanya, tãre da Allah wani abin bautãwa na dabam, lalle nĩ, mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.
Verse 52
Kamar haka dai wani Manzo bai jẽ wa waɗanda ke gabãninsu ba fãce sun ce: "Mai sihiri ne kõ mahaukaci."
Verse 53
shin, sunã yi wa jũna wasiyya da shi ne? Ã'a, sũ dai mutãne ne mãsu girman kai.
Verse 54
ﭧﭨﭩﭪﭫ
ﭬ
Sai ka jũya daga barinsu, kuma kai ba abin zargi ba ne.
Verse 55
ﭭﭮﭯﭰﭱ
ﭲ
Kuma ka tunãtar, dõmin tunãtarwa tanã amfãnin mũminai.
Verse 56
ﭳﭴﭵﭶﭷﭸ
ﭹ
Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini.
Verse 57
Bã Ni nufln (sãmun) wani arziki daga gare su, Bã Ni nufin su (yi Mini hidimar) ciyar da Ni.
Verse 58
Lalle Allah, Shĩ ne Mai azurtãwa, Mai ĩkon yi, Mai cikakken ƙarfi.
Verse 59
To, lalle waɗanda suka yi zãlunci sunã da masaki (na ɗĩban zunubi) kamar masakin abõkansu, sabõda haka kada su yi Mini gaggãwa.
Verse 60
Sabõda haka, bone ya tabbata ga waɗanda suka kãfirta, daga rãnar su wadda aka yi musu alkawari.
تقدم القراءة