Fassarar Surar Al-Buruj a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
Verse 1
ﭛﭜﭝ
ﭞ
Al-Buruj
Inã rantsuwa da sama mai taurãrin lissafin shekara.
Verse 2
ﭟﭠ
ﭡ
Da yinin da aka yi alkawarin zuwansa,
Verse 3
ﭢﭣ
ﭤ
Da yini mai shaidu, da yini da ake halarta a cikinsa
Verse 4
ﭥﭦﭧ
ﭨ
An la'ani mutãnen rãmi.
Verse 5
ﭩﭪﭫ
ﭬ
Wato wuta wadda aka hura.
Verse 6
ﭭﭮﭯﭰ
ﭱ
A lõkacin da suke a kan (gefen) ta a zazzaune.
Verse 7
ﭲﭳﭴﭵﭶﭷ
ﭸ
Alhãli sũ, bisa ga abin da suke aikatãwa ga mũminai, sunã halarce.
Verse 8
Kuma ba su tuhumce su ba, fãce kawai domin sun yi ĩmãni da Allah Mabuwãyi, wanda ake gõdewa.
Verse 9
Wanda Yake shi ne da mulkin sammai da ƙasa, kuma Allah a kan kõme halarce Yake.
Verse 10
Lalle ne waɗanda suka fitini mũminai maza da mũminai mãta, sa'an nan ba su tũba ba to, sunã da azãbar Jahannama, kuma sunã da azãbar gõbara.
Verse 11
Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da gidãjen Aljanna, ƙoramu na gudãna daga ƙarƙashin gidãjen. Wancan abu fa shi ne rabo babba.
Verse 12
ﮮﮯﮰﮱ
ﯓ
Lalle ne damƙar Ubangijinka mai tsanani ce ƙwarai.
Verse 13
ﯔﯕﯖﯗ
ﯘ
Lalle ne Shĩ, Shi ne Mai ƙãga halitta, kuma Ya mayar da ita (bãyan mutuwa).
Verse 14
ﯙﯚﯛ
ﯜ
Kuma Shi ne Mai gãfara, Mai bayyana sõyayya.
Verse 15
ﯝﯞﯟ
ﯠ
Mai Al'arshi mai girma
Verse 16
ﯡﯢﯣ
ﯤ
Mai aikatãwa ga abin da Yake nufi.
Verse 17
ﯥﯦﯧﯨ
ﯩ
Ko lãbãrin rundanõni yã zo maka.
Verse 18
ﯪﯫ
ﯬ
Fir'auna da samũdãwa?
Verse 19
ﯭﯮﯯﯰﯱ
ﯲ
Ã'aha! waɗanda suka kãfirta sunã cikin ƙaryatãwa.
Verse 20
ﯳﯴﯵﯶ
ﯷ
Alhãli, Allah daga bãyansu, Mai kẽwaye su ne (da saninSa).
Verse 21
ﯸﯹﯺﯻ
ﯼ
Ã'aha! Shi Alƙur'ãni ne mai girma.
Verse 22
ﯽﯾﯿ
ﰀ
A cikin Allo tsararre.
تقدم القراءة