Fassarar Surar Al-Balad a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
Verse 1
ﭽﭾﭿﮀ
ﮁ
Al-Balad
Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari ba.
Verse 2
ﮂﮃﮄﮅ
ﮆ
Alhãli kai kanã mai sauka a cikin wannan gari.
Verse 3
ﮇﮈﮉ
ﮊ
Da mahaifi da abin da ya haifa.
Verse 4
ﮋﮌﮍﮎﮏ
ﮐ
Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala.
Verse 5
ﮑﮒﮓﮔﮕﮖ
ﮗ
Kõ yanã zaton bãbu wani mai iya sãmun iko, a kansa?
Verse 6
ﮘﮙﮚﮛ
ﮜ
Yana cẽwa "Na halakarda dũkiya mai yawa,"
Verse 7
ﮝﮞﮟﮠﮡ
ﮢ
Shin, yana zaton cewa wani bai gan shi ba?
Verse 8
ﮣﮤﮥﮦ
ﮧ
Shin, ba Mu sanya masa idãnu biyu ba?
Verse 9
ﮨﮩ
ﮪ
Da harshe, da leɓɓa biyu.
Verse 10
ﮫﮬ
ﮭ
Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyõyi biyu ba?
Verse 11
ﮮﮯﮰ
ﮱ
To, don mene ne bai shiga Aƙabã ba?
Verse 12
ﯓﯔﯕﯖ
ﯗ
Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Aƙabã?
Verse 13
ﯘﯙ
ﯚ
Ita ce fansar wuyan bãwa.
Verse 14
ﯛﯜﯝﯞﯟﯠ
ﯡ
Ko kuwa ciyarwa, a cikin yini ma'abũcin yunwa.
Verse 15
ﯢﯣﯤ
ﯥ
Ga marãya ma'abũcin zumunta.
Verse 16
ﯦﯧﯨﯩ
ﯪ
Ko kuwa wani matalauci ma'abũcin turɓãya.
Verse 17
Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi wa jũna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa jũna wasiyya da tausayi.
Verse 18
ﯵﯶﯷ
ﯸ
Waɗannan ne ma'abũta albarka
Verse 19
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyinMu, sũ ne ma'abũta shu'umci
Verse 20
ﭘﭙﭚ
ﭛ
A kansu akwai wata wuta abar kullewa.
تقدم القراءة