سورة البلد

الترجمة الهوساوية

Fassarar Surar Al-Balad a الهوساوية daga الترجمة الهوساوية

الترجمة الهوساوية

الناشر

مجمع الملك فهد

Verse 1
Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari* ba.
____________________
  * Allah Ya ce ba sai Ya yi rantsuwa da Makka ba, sa'an nan zã a san darajarta a lõkacinda Annabi yake a cikinta, kuma shi yana da haƙƙin zama a cikinta mahaifansa da zurriyarsa duka, ko da yake zai yi hijira sabõda fitinar kãfirai mãsu halaka dũkiyarsu kan adãwa da shi. Dã sun yi amfãni da dukiyar ga ayyukan alheri, dã yã fi musu.
Verse 6
Yana cẽwa "Na* halakarda dũkiya mai yawa,"
____________________
 * Nã halaka dukiya mai yawa dõmin faɗã da addĩni.
Verse 10
Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyõyi* biyu ba?
____________________
* Hanyar alheri da ta sharri.
Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi wa jũna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa jũna wasiyya da tausayi.
Verse 18
Waɗannan ne ma'abũta albarka*
____________________
 * Ko kuwa waɗanda ake bai wa takardunsu da dãma, a Lãhira.
Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyinMu, sũ ne ma'abũta shu'umci(5)
____________________
  (5) Ko kuwa waɗanda ake bai wa takardunsu da hagu, a Lãhira.
تقدم القراءة