Fassarar Surar As-Shu'ara a الهوساوية daga الترجمة الهوساوية
Verse 1
ﭑ
ﭒ
¦. S̃. M̃.
Verse 2
ﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
Waɗancan ãyõyin Littãfi ne bayyananne.
Verse 3
ﭘﭙﭚﭛﭜﭝ
ﭞ
Tsammãninka kai mai zaka halakar da ranka ne, dõn ba su zamanto mũminai ba!
____________________
* Wannan yã nũna cewa Annabi Muhammadu yanã jin tsõron rashin ĩmãnin mutãnensa, kada ya zama shĩ ne ya gajarta daga abin da Allah Ya ɗõra a kansa, na iyar da manzanci. Haka mũmini yake, kullum girman Ubangijinsa yake dũbi, sabõda haka kõme ya yi na ɗã'a, sai ya ga kãsãwar kansa ga tsayuwa da hakkin Ubangijinsa, a kansa, ya ƙãra jin tsõro da tawãli'u.
____________________
* Wannan yã nũna cewa Annabi Muhammadu yanã jin tsõron rashin ĩmãnin mutãnensa, kada ya zama shĩ ne ya gajarta daga abin da Allah Ya ɗõra a kansa, na iyar da manzanci. Haka mũmini yake, kullum girman Ubangijinsa yake dũbi, sabõda haka kõme ya yi na ɗã'a, sai ya ga kãsãwar kansa ga tsayuwa da hakkin Ubangijinsa, a kansa, ya ƙãra jin tsõro da tawãli'u.
Verse 4
Idan Mun so zã Mu saukar, a kansu, da wata ãyã daga sama, sai wuyõyinsu su yini sabõda ita sunã mãsu ƙasƙantar da kai.
Verse 5
Kuma wata tunãtarwa ba ta jẽ musu ba, daga Mai rahama, sãbuwa, fãce sun kasance daga barinta sunã mãsu bijirẽwa.
Verse 6
To, lalle ne, sun ƙaryata, to, lãbãran abin da suka kasance sunã yi na izgili da shi zã ya je musu.
Verse 7
Shin, ba su dũba ba zuwa ga ƙasa, da yawa Muka tsirar a cikinta, daga dukan nau'i mai kyau?
Verse 8
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mũminai ba.
Verse 9
ﮖﮗﮘﮙﮚ
ﮛ
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai rahama.
Verse 10
Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya kirãyi Mũsã, "Ka je wa mutãnen nan azzãlumai.
Verse 11
ﮥﮦﮧﮨﮩ
ﮪ
"Mutãnen Fir'auna bã zã su yi taƙawa ba?"
Verse 12
ﮫﮬﮭﮮﮯﮰ
ﮱ
Ya ce: "Ya Ubangijĩna, nĩ inã tsõron su ƙaryata ni.
Verse 13
"Kuma ƙirjĩna ya yi ƙunci* kuma harshẽna bã zai saku ba sabõda haka ka aika zuwa ga Harũna.
____________________
* Mũsa yanã nũna cewa, shi yanã jin tsõro kada ya zama ya gajarta wajen iyar da manzanci, dõmin shi mai saurin fushine, yanã neman a taimake shi ɗan'uwansa Hãrũna.Wannan ya yi kama da farkon sũrar inda Annabi, tshĩra da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya nũna tsõron taƙaitãwa ga iyar da manzancin Allah zuwa ga mutãnensa dõmin haka ba su yi ĩmãni ba. Hãlin Annabawa duka ɗaya ne ga tsõron taƙaita aikin Ubangijinsu.
____________________
* Mũsa yanã nũna cewa, shi yanã jin tsõro kada ya zama ya gajarta wajen iyar da manzanci, dõmin shi mai saurin fushine, yanã neman a taimake shi ɗan'uwansa Hãrũna.Wannan ya yi kama da farkon sũrar inda Annabi, tshĩra da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya nũna tsõron taƙaitãwa ga iyar da manzancin Allah zuwa ga mutãnensa dõmin haka ba su yi ĩmãni ba. Hãlin Annabawa duka ɗaya ne ga tsõron taƙaita aikin Ubangijinsu.
Verse 14
ﯜﯝﯞﯟﯠﯡ
ﯢ
"Kuma sunã da wani laifi a kaina, sabõda haka inã tsõron kada su kashe ni."
Verse 15
Ya ce: "Kayya! Ku tafi, kũ biyu, da ÃyõyinMu. Lalle ne, Munã tãre da ku Munã Mãsu saurãre."
Verse 16
"Sai ku je wa Fir'auna, sa'an nan ku ce, Lalle ne, mu, Manzannin Ubangijin halitta ne."
Verse 17
ﯵﯶﯷﯸﯹ
ﯺ
"Ka saki Banĩ Isrã'ila tãre da mu."
Verse 18
Ya ce: "Shin, ba mu yi rẽnonka ba a cikinmu kanã jãrĩri, kuma ka zauna a cikinmu shẽkarudaga lõkacin rãyuwarka?"
Verse 19
"Kuma ka aikata aikinka wanda ka aikata alhãli kai kanã daga butulai?"
Verse 20
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
Ya ce: "Na aikata shi a lõkacin inã daga mãsu jãhilcin fushi."
Verse 21
"Sabõda haka na gudu daga gãre ku a lõkacin da na ji tsõronku, sai Ubangijĩna Ya bã ni hukunci, kuma Ya sanya ni daga Manzanni."
Verse 22
"Kuma waccan ni'ima ce, kanã gõrint a kaina, dõmin kã bautar da Banĩ Isrã'ĩla."
Verse 23
ﭭﭮﭯﭰﭱ
ﭲ
Fir'auna ya ce: "Kuma mene ne Ubangijin halittu?"
Verse 24
Ya ce: "Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu ƙarfin ĩmãni."
Verse 25
ﭾﭿﮀﮁﮂ
ﮃ
Ya ce wa waɗanda suke a gẽfensa, "Bã za ku saurãra ba?"
Verse 26
ﮄﮅﮆﮇﮈ
ﮉ
Ya ce: "Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko."
Verse 27
Ya ce: "Lalle ne Manzonku, wanda aka aiko zuwa gare ku, haƙi ƙa, mahaukaci ne."
Verse 28
Ya ce: "Ubangijin mafitar rãnã da maɓũyarta da abin dayake a tsakaninsu, idan kun kasance kunã hankalta."
Verse 29
Ya ce: "Lalle ne idan ka riƙi wani abin bautãwa wanĩna haƙĩƙa, inã sanyã ka daga ɗaurarru."
Verse 30
ﮦﮧﮨﮩﮪ
ﮫ
Ya ce: "Ashe, kuma kõ dã nã zõ maka da wani, abu mai bayyanãwa?"
Verse 31
Ya ce: "To, ka zõ da shi idan ka kasance daga, mãsu gaskiya."
Verse 32
ﯕﯖﯗﯘﯙﯚ
ﯛ
Sai ya jẽfa sandarsa, sai ga ta kumurci bayyananne.
Verse 33
ﯜﯝﯞﯟﯠﯡ
ﯢ
Kuma ya fizge hannunsa, sai ga shi fari ga mãsu kallo.
Verse 34
(Fir'auna) ya ce ga mashãwarta a gẽfensa, "Lalle ne, wannan haƙĩƙa, masihirci ne, mai ilmi!
Verse 35
"Yanã son ya fitar da ku daga ƙasarku game da sihirinSa. To mẽne ne kuke shãwartãwa?"
Verse 36
Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shĩ da ɗan'uwansa, kuma ka aika mãsu gayya a cikin birãne."
Verse 37
ﯼﯽﯾﯿ
ﰀ
"Zã su zõ maka da dukkan mai yawan sihiri masani."
Verse 38
ﰁﰂﰃﰄﰅ
ﰆ
Sai aka tãra masihirta dõmin ajalin yini sananne.
Verse 39
ﰇﰈﰉﰊﰋ
ﰌ
Kuma aka ce wa mutãne "Kõ kũ mãsu tãruwã ne?
Verse 40
"Tsammãninmu mu bi masihirta, idan sun kasance sũ ne marinjãya."
Verse 41
To, a lõkacin da masihirta suka jẽ suka ce wa Fir'auna,"Shin, lalle ne, haƙĩƙa munã da ijãra idan mun kasance mũ ne marinjãya?"
Verse 42
ﭦﭧﭨﭩﭪﭫ
ﭬ
Ya ce: "Na'am! Kuma lalle ne, kũ ne a lõkacin haƙĩƙa muƙarrabai."
Verse 43
Mũsã ya ce musu, "Ku jẽfa abin da kuke mãsu jẽfãwa."
Verse 44
Sai suka jẽfa igiyõyinsu, da sandunansu, kuma suka ce: "Da ƙarfin Fir'auna lalle ne mũ, haƙĩƙa, mũ ne marinjãya."
Verse 45
Sai Mũsa ya jẽfa sandarsa, sai ga ta tanã harhaɗe abin da suke yi na ƙarya.
Verse 46
ﮈﮉﮊ
ﮋ
Sai aka jẽfar da masihirta sunã mãsu sujada.
Verse 47
ﮌﮍﮎﮏ
ﮐ
Suka ce: "Mun yi ĩmãni da Ubangijin halitta."
Verse 48
ﮑﮒﮓ
ﮔ
"Ubangijin Mũsa da Hãrũna."
Verse 49
Ya ce: "Ashe, kun yi ĩmãni sabõda shĩ, a gabãnin in yi muku izni? Lalle ne shi, haƙĩƙa babbanku ne wanda ya kõya muku sihirin, to, zã ku sani. Lalle ne haƙĩƙa, zan kakkãtse hannuwanku da kafãfunku a tarnaƙi, kuma haƙĩƙa, zan tsĩrẽ ku gabã ɗaya."
Verse 50
Suka ce: "Bãbu wata cũta! Lalle ne mũ mãsu jũyãwa ne zuwa ga Ubangijinmu."
Verse 51
"Lalle ne mu munã kwaɗayin Ubangijinmu, Ya gãfarta mana kurakuranmu dõmin mun kasance farkon mãsu ĩmãni."
Verse 52
Kuma Muka aika zuwa ga Mũsã cẽwa ka yi tafiyar dare da bãyiNa, lalle ne kũ waɗanda ake biyã* ne.
____________________
* Mũsa yanã nũna cewa, shi yanã jin tsõro kada ya zama ya gajarta wajen iyar da manzanci, dõmin shi mai saurin fushine, yanã neman a taimake shi ɗan'uwansa Hãrũna.Wannan ya yi kama da farkon sũrar inda Annabi, tshĩra da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya nũna tsõron taƙaitãwa ga iyar da manzancin Allah zuwa ga mutãnensa dõmin haka ba su yi ĩmãni ba. Hãlin Annabawa duka ɗaya ne ga tsõron taƙaita aikin Ubangijinsu.
____________________
* Mũsa yanã nũna cewa, shi yanã jin tsõro kada ya zama ya gajarta wajen iyar da manzanci, dõmin shi mai saurin fushine, yanã neman a taimake shi ɗan'uwansa Hãrũna.Wannan ya yi kama da farkon sũrar inda Annabi, tshĩra da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya nũna tsõron taƙaitãwa ga iyar da manzancin Allah zuwa ga mutãnensa dõmin haka ba su yi ĩmãni ba. Hãlin Annabawa duka ɗaya ne ga tsõron taƙaita aikin Ubangijinsu.
Verse 53
ﯭﯮﯯﯰﯱ
ﯲ
Sai Fir'auna ya aika mãsu gayya a cikin birãne.
Verse 54
ﯳﯴﯵﯶ
ﯷ
"Lalle ne, waɗannan, haƙĩƙa, ƙungiya ce kaɗan."
Verse 55
ﯸﯹﯺ
ﯻ
"Kuma lalle ne sũ, a gare Mu, Mãsu fusãtarwa ne."
Verse 56
ﯼﯽﯾ
ﯿ
"Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa gabã ɗaya mãsu sauna ne."
Verse 57
ﰀﰁﰂﰃ
ﰄ
Sai Muka fitar da su daga gonaki da marẽmari.
Verse 58
ﰅﰆﰇ
ﰈ
Da taskõki da mazauni mai kyau.
Verse 59
ﰉﰊﰋﰌﰍ
ﰎ
Kamar haka! Kuma Muka gãdar da su ga Banĩ Isrãĩla.
Verse 60
ﰏﰐ
ﰑ
Sai suka bĩ su sunã mãsu fita a lõkacin hũdõwar rãnã.
Verse 61
Sa'an nan a lõkacin da jama'a biyu suka ga jũna, sai abõkan Mũsã suka ce: "Lalle ne mũ haƙĩ ƙa, waɗanda ake riska ne."
Verse 62
Ya ce: "Kayya! Lalle ne Ubangijina Yanã tare da ni, zai shiryar da ni."
Verse 63
Sai Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã cẽwa "Ka dõki tẽku da sandarka." Sai tẽku ta tsãge,* kõwane tsãgi ya kasance kamar falalen dũtse mai girma.
____________________
* Teku ta tsãge hanya gõma sha biyu a kan adadin danginBanĩ Isrãĩla. Suka bi suka wuce, sa'ilin nan aka nutsar daFir'auna, shi da jama'arsa, a cikin hanyõyin ruwan,.
____________________
* Teku ta tsãge hanya gõma sha biyu a kan adadin danginBanĩ Isrãĩla. Suka bi suka wuce, sa'ilin nan aka nutsar daFir'auna, shi da jama'arsa, a cikin hanyõyin ruwan,.
Verse 64
ﭱﭲﭳ
ﭴ
Kuma Muka kusantar da waɗansu mutãne a can.
Verse 65
ﭵﭶﭷﭸﭹ
ﭺ
Kuma Muka tsĩrar da Mũsã da waɗanda suke tãre da shi gabã ɗaya.
Verse 66
ﭻﭼﭽ
ﭾ
Sa'an nan kuma Muka nutsar da waɗansu mutãnen.
Verse 67
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
Verse 68
ﮉﮊﮋﮌﮍ
ﮎ
Kuma lalle ne Ubangijinka, kaƙĩƙa, Shĩ ne Mabũwayi, Mai jin ƙai.
Verse 69
ﮏﮐﮑﮒ
ﮓ
Kuma ka karanta, a kansu, lãbãrin Ibrãhĩm.
Verse 70
ﮔﮕﮖﮗﮘﮙ
ﮚ
A sã'ilin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bauta wa?"
Verse 71
ﮛﮜﮝﮞﮟﮠ
ﮡ
Suka ce: "Munã bauta wa gumãka, sabõda haka munã yini mãsu lazimta a gare su."
Verse 72
ﮢﮣﮤﮥﮦ
ﮧ
Ya ce: "Shin, sunã jin ku, a lõkacin da kuke kira?"
Verse 73
ﮨﮩﮪﮫ
ﮬ
"Kõ kuwa sunã amfãnin ku, kõ sunã cũtar ku?"
Verse 74
ﮭﮮﮯﮰﮱﯓ
ﯔ
Suka ce: "Ã'a mun sãmĩ ubanninmu, kamar haka ne suke aikatãwa."
Verse 75
ﯕﯖﯗﯘﯙ
ﯚ
Ya ce: "Shin to, kun ga abin da kuka kasance kunã bautã wa?"
Verse 76
ﯛﯜﯝ
ﯞ
"Kũ da ubanninku mafi daɗẽwa?"
Verse 77
ﯟﯠﯡﯢﯣﯤ
ﯥ
"To lalle ne, sũ maƙiya ne a gare ni, fãce Ubangijin halittu."
Verse 78
ﯦﯧﯨﯩ
ﯪ
"Wanda Ya halitta ni, sa'an nan Yanã shiryar da ni."
Verse 79
ﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
"Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni."
Verse 80
ﯰﯱﯲﯳ
ﯴ
"Kuma idan na yi jiyya, to, Shĩ ne Yake warkar da ni."
Verse 81
ﯵﯶﯷﯸ
ﯹ
"Kuma wanda Yake matar da ni, sa'an nan Ya rãyar da ni."
Verse 82
"Kuma wanda Yake inã kwaɗayin Ya gãfarta mini kurãkuraina, a rãnar sãkamako."
Verse 83
ﰃﰄﰅﰆﰇﰈ
ﰉ
"Ya Ubangijĩna! Ka ba ni hukunci, kuma Ka riskar da ni ga sãlihai."
Verse 84
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
"Kuma Ka sanya mini harshen gaskiya* a cikin mutãnen ƙarshe."
____________________
* Harshen gaskiya shĩ ne yabõ mai kyau. Mutãnen ƙarshe sũ ne Musulmi al'ummar Annabi Muhammadu, mãsu shaida ga annabawa da iyar da manzanci
____________________
* Harshen gaskiya shĩ ne yabõ mai kyau. Mutãnen ƙarshe sũ ne Musulmi al'ummar Annabi Muhammadu, mãsu shaida ga annabawa da iyar da manzanci
Verse 85
ﭘﭙﭚﭛﭜ
ﭝ
"Kuma Ka sanya ni daga magãdan Aljannar ni'ima."
Verse 86
ﭞﭟﭠﭡﭢﭣ
ﭤ
"Kuma Ka gãfarta wa ubãna, lalle ne shi, ya kasance daga ɓatattu."
Verse 87
ﭥﭦﭧﭨ
ﭩ
"Kuma kada Ka kunyata ni a rãnar da ake tãyar da su."
Verse 88
ﭪﭫﭬﭭﭮﭯ
ﭰ
"A rãnar da dũkiya bã ta amfãni, kuma ɗiya bã su yi."
Verse 89
ﭱﭲﭳﭴﭵﭶ
ﭷ
"Fãce wanda ya jẽ wa Allah da zũciya mai tsarki."
Verse 90
ﭸﭹﭺ
ﭻ
Kuma aka kusantar da Aljanna ga mãsu taƙawa.
Verse 91
ﭼﭽﭾ
ﭿ
Kuma aka fitar da wutã babba dõmin halakakku.
Verse 92
ﮀﮁﮂﮃﮄﮅ
ﮆ
Kuma aka ce musu, "Inã abin da kuka kasance kunã bautawa?"
Verse 93
"Baicin Allah? Shin sunã tamakon ku kõ kuwa sunã tsare kansu?"
Verse 94
ﮏﮐﮑﮒ
ﮓ
Sai aka kikkife su* a cikinta, su da halakakkun.
____________________
* Gumãkan, sũ da halakakku mabiyansu. Dukkan mai ɓatarda wani shĩ ne gunki ga mai bin sa halakakke.
____________________
* Gumãkan, sũ da halakakku mabiyansu. Dukkan mai ɓatarda wani shĩ ne gunki ga mai bin sa halakakke.
Verse 95
ﮔﮕﮖ
ﮗ
Da rundunar Ibilĩsa gabã ɗaya.
Verse 96
ﮘﮙﮚﮛ
ﮜ
Suka ce: alhãli sunã a cikinta sunã yin husũma,
Verse 97
ﮝﮞﮟﮠﮡﮢ
ﮣ
"Rantsuwa da Allah! Lalle ne mun kasance, haƙĩƙa, a cikin ɓata bayyananna."
Verse 98
ﮤﮥﮦﮧ
ﮨ
"A lõkacin da muke daidaita ku da Ubangijin halittu.
Verse 99
ﮩﮪﮫﮬ
ﮭ
"Kuma bãbu abin da ya ɓatar da mu fãce mãsu laifi."
Verse 100
ﮮﮯﮰﮱ
ﯓ
"Sabõda haka bã mu da waɗansu macẽta."
Verse 101
ﯔﯕﯖ
ﯗ
"Kuma bã mu da abõki, masõyi."
Verse 102
"Sabõda haka dã lalle munã da (dãmar) kõmawa, dõmin mu kasance daga mũminai!"
Verse 103
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, bã su kasance mũminai ba.
Verse 104
ﯪﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
Kuma lalle ne, Ubangijinka, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
Verse 105
ﯰﯱﯲﯳ
ﯴ
Mutãnen Nũhu sun ƙaryata Manzanni.
Verse 106
A lõkacin da Dan uwansu Nuhu ya ce musu, "Bã zã ku ji tsoron Allah ba?"
Verse 107
ﯽﯾﯿﰀ
ﰁ
"Lalle ne, zuwa gare ku, ni Manzo ne amintacce."
Verse 108
ﰂﰃﰄ
ﰅ
"To, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Verse 109
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãtã ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
Verse 110
ﰓﰔﰕ
ﰖ
"Sabõda haka, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Verse 111
ﰗﰘﰙﰚﰛﰜ
ﰝ
Suka ce: "Ashe, zã mu yi ĩmãni sabõda kai alhãli kuwa mafiya ƙasƙanci sun bi ka?"
Verse 112
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
Ya ce: "Kuma bã ni da sani ga abin da suka kasance sanã aikatãwa."
Verse 113
"Hisãbinsu bai zama ba fãce ga Ubangijina, dã kunã sansancẽwa."
Verse 114
ﭡﭢﭣﭤ
ﭥ
"Ban zama mai kõre mũminai ba."
Verse 115
ﭦﭧﭨﭩﭪ
ﭫ
"Nĩ ba kõwa ba ne sai mai gargaɗi mai bayyanãwa."
Verse 116
Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, yã Nũhu, (daga maganarka,) haƙĩƙa, kanã kasancẽwa daga waɗanda ake jẽfewa"
Verse 117
ﭵﭶﭷﭸﭹ
ﭺ
Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Lalle ne mutãnena sun ƙaryatã ni."
Verse 118
"Sai ka yi hukunci, a tsakãnĩna da tsakãninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsĩrar da ni, da waɗanda suke tãre da ni daga mũminai."
Verse 119
ﮅﮆﮇﮈﮉﮊ
ﮋ
Sai Muka tsĩrar da shi, shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lõdi.
Verse 120
ﮌﮍﮎﮏ
ﮐ
Sa'an nan Muka nutsar a bãyan haka, da sauran.
Verse 121
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
Verse 122
ﮛﮜﮝﮞﮟ
ﮠ
Kuma Lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai Rahama.
Verse 123
ﮡﮢﮣ
ﮤ
Ãdãwa sun ƙaryata Manzanni.
Verse 124
A lõkacin da ɗan'uwansu, Hũdu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
Verse 125
ﮭﮮﮯﮰ
ﮱ
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, haƙĩƙa, Manzo ne, amintacce."
Verse 126
ﯓﯔﯕ
ﯖ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Verse 127
"Kuma bã ni tambayar wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba, fãce daga Ubangijin halittu."
Verse 128
ﯤﯥﯦﯧﯨ
ﯩ
"Shin, kunã yin ginin sitadiyo* a kõwane tsauni ne, kunã yin wãsa?"
____________________
* Sitãdiyo shi ne gidan wasanni da Turanci, alãmã da Lãrabci.
____________________
* Sitãdiyo shi ne gidan wasanni da Turanci, alãmã da Lãrabci.
Verse 129
ﯪﯫﯬﯭ
ﯮ
"Kuma kunã riƙon matsãrar ruwa, tsammãninku, ku dawwama?*"
____________________
* Kõ kuma wurãren sanã'õ'i kamar masãƙoƙi irin na zãmanin nan.
____________________
* Kõ kuma wurãren sanã'õ'i kamar masãƙoƙi irin na zãmanin nan.
Verse 130
ﯯﯰﯱﯲ
ﯳ
"Kuma idan kun yi damƙa, sai ku yi damƙar kunã mãsu tanƙwasãwa."
Verse 131
ﯴﯵﯶ
ﯷ
"To ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Verse 132
ﯸﯹﯺﯻﯼ
ﯽ
"Ku ji tsõron wanda Ya taimake ku da abin da kuka sani."
Verse 133
ﯾﯿﰀ
ﰁ
"Ya taimake ku da dabbõbin ni'ima da ɗiya."
Verse 134
ﰂﰃ
ﰄ
"Da gõnaki da marẽmari."
Verse 135
ﰅﰆﰇﰈﰉﰊ
ﰋ
"Lalle ne nĩ, inã ji muku tsõron azãbar wani yini mai girma."
Verse 136
Suka ce: "Daidai ne a kanmu: Kã yi wa'azi kõ ba ka kasance daga mãsu wa'azi ba."
Verse 137
ﭑﭒﭓﭔﭕ
ﭖ
"Wannan abu bai zamõ ba fãce hãlãyen* mutãnen farko."
____________________
* Wãtau lãbarun mutãne waɗanda ba su ci gaba ba bã su son a yi rawa da nishãɗi. Anã karantawar ma'anar ƙaryar ta farko, watau wai tãtsũniya ce: a ce wai a hana ãyã akan tsaunuka dõmin wasanni. Suna nufi da ãya ko alãma gidãjen rawa da na nashãdi watau stadiyam da kasĩno.
____________________
* Wãtau lãbarun mutãne waɗanda ba su ci gaba ba bã su son a yi rawa da nishãɗi. Anã karantawar ma'anar ƙaryar ta farko, watau wai tãtsũniya ce: a ce wai a hana ãyã akan tsaunuka dõmin wasanni. Suna nufi da ãya ko alãma gidãjen rawa da na nashãdi watau stadiyam da kasĩno.
Verse 138
ﭗﭘﭙ
ﭚ
"Kuma mũ ba mu zama waɗanda ake yi wa azãba ba."
Verse 139
Sabõda haka suka ƙaryata shi, sai Muka halakar da sũ. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
Verse 140
ﭨﭩﭪﭫﭬ
ﭭ
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
Verse 141
ﭮﭯﭰ
ﭱ
Samũdãwa sun ƙaryata Manzanni.
Verse 142
A lõkacin da ɗan'uwansu Sãlihu ya ce: "Shin, bã zã ku bi Allah da taƙawa ba?"
Verse 143
ﭺﭻﭼﭽ
ﭾ
"Lalle ne nĩ zuwã gare ku, Manzo ne, amintacce."
Verse 144
ﭿﮀﮁ
ﮂ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã.
Verse 145
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba fãce da a Ubangijin halittu."
Verse 146
ﮐﮑﮒﮓﮔ
ﮕ
"Shin, anã barin ku* a cikin abin da yake a nan, kunã amintattu?"
____________________
* Kuna zaton zã a bar ku a irin wannan ni'ima' Allah bã zai karɓi rãyukanku ba kuma Ya yi muku hisãbi a kanta? Kayya! Zã a yi muku hisãbi a bãyan kun mutu an tsayar da ku, dõmin hisãbin ayyukan da kuka yi.
____________________
* Kuna zaton zã a bar ku a irin wannan ni'ima' Allah bã zai karɓi rãyukanku ba kuma Ya yi muku hisãbi a kanta? Kayya! Zã a yi muku hisãbi a bãyan kun mutu an tsayar da ku, dõmin hisãbin ayyukan da kuka yi.
Verse 147
ﮖﮗﮘ
ﮙ
"A cikin gõnaki da marẽmari."
Verse 148
ﮚﮛﮜﮝ
ﮞ
"Da shuke-shuke da dabĩ nai, 'ya'yan itãcensu hirtsi* mãsu narkẽwa a ciki?"
____________________
* Hirtsi shi ne 'ya'yan itãce sãbabbi tun ba su nuna ba. Wãtau hirtsin gonakinsu idan an ci shi narkewã ya ke yi a cikin ciki, balle kuma 'ya'yan itãce nunannu.
____________________
* Hirtsi shi ne 'ya'yan itãce sãbabbi tun ba su nuna ba. Wãtau hirtsin gonakinsu idan an ci shi narkewã ya ke yi a cikin ciki, balle kuma 'ya'yan itãce nunannu.
Verse 149
ﮟﮠﮡﮢﮣ
ﮤ
"Kuma kunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, kunã mãsu alfãhari?"
Verse 150
ﮥﮦﮧ
ﮨ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Verse 151
ﮩﮪﮫﮬ
ﮭ
"Kada ku yi ɗã'ã ga umurnin maɓarnata."
Verse 152
ﮮﮯﮰﮱﯓﯔ
ﯕ
"Waɗanda suke yin ɓarna a cikin ƙasa, kuma bã su kyautatãwa."
Verse 153
ﯖﯗﯘﯙﯚ
ﯛ
Suka ce: "Kai daga mãsu sihiri kurum kake."
Verse 154
"Bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu. To, kã zo da wata ãyã idan kã kasance daga mãsu gaskiya."
Verse 155
Ya ce: "Wannan rãkuma ce tanã da shan* yini, kuma kunã da shan yini sasanne."
____________________
* Kuna zaton zã a bar ku a irin wannan ni'ima' Allah bã zai karɓi rãyukanku ba kuma Ya yi muku hisãbi a kanta? Kayya! Zã a yi muku hisãbi a bãyan kun mutu an tsayar da ku, dõmin hisãbin ayyukan da kuka yi.
____________________
* Kuna zaton zã a bar ku a irin wannan ni'ima' Allah bã zai karɓi rãyukanku ba kuma Ya yi muku hisãbi a kanta? Kayya! Zã a yi muku hisãbi a bãyan kun mutu an tsayar da ku, dõmin hisãbin ayyukan da kuka yi.
Verse 156
"Kada ku shãfe ta da cũta har azãbar yini mai girmã ta shãfe ku."
Verse 157
ﯺﯻﯼ
ﯽ
Sai suka sõke ta sa'an nan suka wãyi gari sunã mãsu nadãma.
Verse 158
Sabõda haka azãba ta kãma su. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
Verse 159
ﰋﰌﰍﰎﰏ
ﰐ
Lalle ne Ubangijinka, haƙĩ ƙa, Shĩ ne Mabuwayi, Mai jin ƙai.
Verse 160
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata Manzanni.
Verse 161
A lõkacin da ɗan'uwansu,* Lũɗu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
____________________
* Lũɗu ɗan'uwansu ne na zaman gari da aure kawai. Asalinsa ɗan baffan Ibrãhĩm ne, sun tãso daga gabas, ƙasar Bãbila suka yi hijira, har ibrahĩm ya sauka Habrũna a ƙasar Shãm, Lũɗu kuwa ya sauka a sadũm da alƙaryunta.
____________________
* Lũɗu ɗan'uwansu ne na zaman gari da aure kawai. Asalinsa ɗan baffan Ibrãhĩm ne, sun tãso daga gabas, ƙasar Bãbila suka yi hijira, har ibrahĩm ya sauka Habrũna a ƙasar Shãm, Lũɗu kuwa ya sauka a sadũm da alƙaryunta.
Verse 162
ﭞﭟﭠﭡ
ﭢ
"Lalle ne nĩ, zuwa gare ku, Manzõ ne, amintacce."
Verse 163
ﭣﭤﭥ
ﭦ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Verse 164
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra, Ijãrãta ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
Verse 165
ﭴﭵﭶﭷ
ﭸ
"Shin kunã jẽ wa maza daga cikin talikai?"
Verse 166
"Kuma kunã barin abin da Ubangijinku Ya halitta muku daga mãtanku? Ã'a, ku mutãne ne mãsu ƙẽtarẽwa!"
Verse 167
Suka ce: "Lalle ne haƙĩƙa idan ba ka hanu ba, yã Lũɗu! Tĩlas ne kanã kasancẽwa daga waɗanda ake fitarwa (daga gari)."
Verse 168
ﮏﮐﮑﮒﮓ
ﮔ
Ya ce: "Lalle ne ga aikinku, haƙĩƙa, inã daga mãsu ƙinsa."
Verse 169
ﮕﮖﮗﮘﮙ
ﮚ
"Ya Ubangijina! Ka tsĩrar da ni da iyãlĩna daga abin da suke aikatãwa."
Verse 170
ﮛﮜﮝ
ﮞ
Sabõda haka Muka tsĩrar da shi, Shi da mutãnensa gabã ɗaya.
Verse 171
ﮟﮠﮡﮢ
ﮣ
Fãce wata tsõhuwa a cikin mãsu wanzuwa.
Verse 172
ﮤﮥﮦ
ﮧ
Sa'an nan kuma Muka hallaka wasu.
Verse 173
Kuma Muka yi ruwan sama a kansu ruwa, sai dai ruwan waɗanda ake yi wa gargaɗi ya mũnana.
Verse 174
Lalle ne ga wannan, akwai ãyã, kuma mafi yawansu bã su kasance mãsu ĩmãni ba.
Verse 175
ﯛﯜﯝﯞﯟ
ﯠ
Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
Verse 176
ﯡﯢﯣﯤ
ﯥ
Ma'abũta ƙunci sun ƙaryata Manzanni.
Verse 177
ﯦﯧﯨﯩﯪﯫ
ﯬ
A lõkacin da Shu'aibu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
Verse 178
ﯭﯮﯯﯰ
ﯱ
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, Manzo ne, amintacce."
Verse 179
ﯲﯳﯴ
ﯵ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa kuma ku yi mini ɗã'ã."
Verse 180
"Kuma ba ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrata ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
Verse 181
"Ku cika mũdu, kuma kada ku kasance daga mãsu sanyãwar hasãra (ga mutãne)."
Verse 182
ﰋﰌﰍ
ﰎ
"Kuma ku yi awo da sikẽli daidaitacce."
Verse 183
"Kuma kada ku nakasa wa mutãne abũbuwansu kuma kada ku yi fasãdi a cikin ƙasa kuna mãsu ɓarna."
Verse 184
ﭑﭒﭓﭔﭕ
ﭖ
"Kuma ku ji tsõron Allah wanda Ya halitta ku, kũ da jama'ar farko."
Verse 185
ﭗﭘﭙﭚﭛ
ﭜ
Suka ce: "Kai dai daga waɗanda suke sihirtattu kawai ne."
Verse 186
"Kuma bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu kuma lalle ne munã zaton ka, haƙĩƙa, daga maƙaryata."
Verse 187
"To ka jẽfo wani ɓaɓɓake daga sama a kanmu, idan ka kasance daga mãsu gaskiya."
Verse 188
ﭱﭲﭳﭴﭵ
ﭶ
Ya ce: "Ubangijĩna ne Mafi sani ga abin da kuke aikatãwa."
Verse 189
Sai suka ƙaiyatã shi, sabõda haka, azãbar rãnar girgije* ta kãma su. Lalle ne ita, tã kasance azãbar yini mai girma.
____________________
* An ruwaito cewa Allah Ya bũɗe musu ƙõfar Jahannama, zãfi ya hana su zama akõ'ina cikin gidãjensu, sa'an nan aka sanya girgije ya yi musu inuwa mai sanyi-sanyi har suka tãru a ciki, sa'an nan aka sanya girgijen ya kãma da wuta a kansu suka ƙõne kurmus kamar an gasa fãra. Suka kõma tõka kamar yadda suka nema daga Shu'aibu da a jefa musu ɓaɓɓake daga sama idan ya zama daga mãsu gaskiya.
____________________
* An ruwaito cewa Allah Ya bũɗe musu ƙõfar Jahannama, zãfi ya hana su zama akõ'ina cikin gidãjensu, sa'an nan aka sanya girgije ya yi musu inuwa mai sanyi-sanyi har suka tãru a ciki, sa'an nan aka sanya girgijen ya kãma da wuta a kansu suka ƙõne kurmus kamar an gasa fãra. Suka kõma tõka kamar yadda suka nema daga Shu'aibu da a jefa musu ɓaɓɓake daga sama idan ya zama daga mãsu gaskiya.
Verse 190
Lalle a cikin wancan haƙĩka akwai ãya, amma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
Verse 191
ﮍﮎﮏﮐﮑ
ﮒ
Kuma lalle Ubangijĩnka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
Verse 192
ﮓﮔﮕﮖ
ﮗ
Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne.
Verse 193
ﮘﮙﮚﮛ
ﮜ
Rũhi* amintacce ne ya sauka da shi.
____________________
* Rũhul Ƙudus, shi ne Jibirĩl, amincin Allah ya tabbata a gare shi.
____________________
* Rũhul Ƙudus, shi ne Jibirĩl, amincin Allah ya tabbata a gare shi.
Verse 194
ﮝﮞﮟﮠﮡ
ﮢ
A kan zũciyarka, dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi.
Verse 195
ﮣﮤﮥ
ﮦ
Da harshe na Larabci mai bayãni.
Verse 196
ﮧﮨﮩﮪ
ﮫ
Kuma lalle shin, haƙĩƙa, yanã a cikin litattafan (Manzannin) farko.
Verse 197
Ashe, bai kasance ãyã ba a gare su, ya zama Mãlaman Banĩ Isrã'ĩla sun san shi?
Verse 198
ﯗﯘﯙﯚﯛ
ﯜ
Kuma dã mun saukar da shi a kan sãshen Ajamãwa,
Verse 199
ﯝﯞﯟﯠﯡﯢ
ﯣ
Ya karanta shi a kansu, ba su kasance sabõda shi mãsu ĩmãni ba.
Verse 200
ﯤﯥﯦﯧﯨ
ﯩ
Kamar wancan ne! Muka shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.
Verse 201
Bã zã su yi ĩmãni da shĩ ba sai sun ga azãbar nan mai raɗadi.
Verse 202
ﯲﯳﯴﯵﯶ
ﯷ
Sai ta taho musu kwatsam, alhãli kuwa sũ, ba su sansance ba.
Verse 203
ﯸﯹﯺﯻ
ﯼ
Sai su ce: "Shin, mu waɗanda ake yi wa jinkiri ne?"
Verse 204
ﯽﯾ
ﯿ
Ashe, to, da azãbarMu suke nẽman gaggãwa?
Verse 205
ﰀﰁﰂﰃ
ﰄ
Ashe, to, kã gani, idan Muka jĩshe su daɗi a shẽkaru,
Verse 206
ﰅﰆﰇﰈﰉ
ﰊ
Sa'an nan abin da suka kasance anã yi musu wa'adi (da shi) ya jẽ musu,
Verse 207
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
Abin da suka kasance anã jĩshe su dãɗin bã zai tunkuɗe azãba ba daga gare* su.
____________________
* Dã an bã su lõkaci mai tsawo sunã jin dãɗi da rãyuwar dũniya a cikinsa, to, rãnar da mutuwa kõ azãbar Allah ta je gare su, wannan lõkacin bã zai tunkuɗe mutuwar kõ azabar ba daga gare su.
____________________
* Dã an bã su lõkaci mai tsawo sunã jin dãɗi da rãyuwar dũniya a cikinsa, to, rãnar da mutuwa kõ azãbar Allah ta je gare su, wannan lõkacin bã zai tunkuɗe mutuwar kõ azabar ba daga gare su.
Verse 208
Kuma bã Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da mãsu gargaɗi.
Verse 209
ﭠﭡﭢﭣ
ﭤ
Dõmin tunãtarwa, kuma ba Mu kasance Mãsu zãlunci ba.
Verse 210
ﭥﭦﭧﭨ
ﭩ
Kuma (Alƙur'ãni) Shaiɗãnu ba su ɗõra sauka da shĩba.
Verse 211
ﭪﭫﭬﭭﭮ
ﭯ
Kuma bã ya kamãta a gare su (su Shaiɗãnu su sauka da shi), kuma ba su iyãwa.
Verse 212
ﭰﭱﭲﭳ
ﭴ
Lalle ne sũ, daga saurãre, haƙĩƙa, waɗanda aka nĩsantar ne.
Verse 213
Sabõda haka, kada ka kira wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah, sai ka kasance daga waɗanda ake yi wa azãba.
Verse 214
ﭿﮀﮁ
ﮂ
Kuma ka yi gargaɗi ga danginka mafiya kusanci.
Verse 215
ﮃﮄﮅﮆﮇﮈ
ﮉ
Kuma ka sassauta fikãfikanka* ga wanda ya bĩ ka daga mũminai.
____________________
* Ka zama mai tausayi ga mũminai waɗanda suka bĩ ka, ka yi musu kamar yadda kãzã take yi wa 'ya'yanta ƙanana a lõkacin sanyi, kõ kuwa idan zã su yi barci dõmin ta kãre su daga cũta.
____________________
* Ka zama mai tausayi ga mũminai waɗanda suka bĩ ka, ka yi musu kamar yadda kãzã take yi wa 'ya'yanta ƙanana a lõkacin sanyi, kõ kuwa idan zã su yi barci dõmin ta kãre su daga cũta.
Verse 216
Sa'an nan idan suka sãɓã maka to ka ce: "Lalle nĩ, barrantacce ne daga abin da kuko aikatãwa."
Verse 217
ﮒﮓﮔﮕ
ﮖ
Kuma ka dõgara ga Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
Verse 218
ﮗﮘﮙﮚ
ﮛ
Wanda Yake ganin ka a lõkacin da kake tãshi tsaye.
Verse 219
ﮜﮝﮞ
ﮟ
Da jujjuyãwarka a cikin mãsu yin sujada.
Verse 220
ﮠﮡﮢﮣ
ﮤ
Lalle Shi, Shi* ne Mai ji, Masani.
____________________
* Allah Shi ne Mai ji, ji na gaskiya, kuma Masani, sani na gaskiya.
____________________
* Allah Shi ne Mai ji, ji na gaskiya, kuma Masani, sani na gaskiya.
Verse 221
ﮥﮦﮧﮨﮩﮪ
ﮫ
Shin, (kunã so) in gaya* muku a kan wanda Shaiɗãnnu kan sauka?
____________________
* Wannan dõmin raddi ne gamãsu cewa aljannu ke gayawa Muhammadu, tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi, Alƙur'ãni. Aljannu bã su saukã sai ga maƙaryaci, mai zunubi' Muhammadu kuwa bã haka yake ba. Sabõda haka shi bã mahaukaci ba, kuma ba wanda aljannu suke gaya wa ba. Dukan abin da ya faɗa, to, wahayi ne daga Allah.
____________________
* Wannan dõmin raddi ne gamãsu cewa aljannu ke gayawa Muhammadu, tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi, Alƙur'ãni. Aljannu bã su saukã sai ga maƙaryaci, mai zunubi' Muhammadu kuwa bã haka yake ba. Sabõda haka shi bã mahaukaci ba, kuma ba wanda aljannu suke gaya wa ba. Dukan abin da ya faɗa, to, wahayi ne daga Allah.
Verse 222
ﮬﮭﮮﮯﮰ
ﮱ
Sukan sauka a kan dukkan maƙaryaci, mai zunubi.
Verse 223
ﯓﯔﯕﯖ
ﯗ
Sunã jẽfa (abin da suka) ji, alhãli kuwa mafi yawansu maƙaryata ne.
Verse 224
ﯘﯙﯚ
ﯛ
Kuma mawãƙa(5) halakakku ne ke bin su.
____________________
(5) Siffõfin mawãƙa sun nũna cewa Annabi Muhammadu bã mawãƙi ba ne, dõmin bã shi da ɗaya daga cikin siffõfin mawãƙa. Kuma mabiyansa ba halakakku ba ne.
____________________
(5) Siffõfin mawãƙa sun nũna cewa Annabi Muhammadu bã mawãƙi ba ne, dõmin bã shi da ɗaya daga cikin siffõfin mawãƙa. Kuma mabiyansa ba halakakku ba ne.
Verse 225
Shin, ba ku cẽwa, lalle ne sũ, cikin kõwane rango sunã yin ɗimuwa (su ƙẽtare haddi) ba?
Verse 226
ﯤﯥﯦﯧﯨ
ﯩ
Kuma lalle ne, sũ, sunã faɗin abin da bã su aikatãwa?
Verse 227
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka ambaci Allah da yawa, kuma suka rãma zãlunci, daga bãyan an zãlunce su. Kuma waɗanda suka yi zãlunci, zã su sani a wace majũya suke jũyãwa.
تقدم القراءة