سورة الشعراء

الترجمة الهوساوية

Fassarar Surar As-Shu'ara a الهوساوية daga الترجمة الهوساوية

الترجمة الهوساوية

الناشر

مجمع الملك فهد

Tsammãninka kai mai zaka halakar da ranka ne, dõn ba su zamanto mũminai ba!
____________________
 * Wannan yã nũna cewa Annabi Muhammadu yanã jin tsõron rashin ĩmãnin mutãnensa, kada ya zama shĩ ne ya gajarta daga abin da Allah Ya ɗõra a kansa, na iyar da manzanci. Haka mũmini yake, kullum girman Ubangijinsa yake dũbi, sabõda haka kõme ya yi na ɗã'a, sai ya ga kãsãwar kansa ga tsayuwa da hakkin Ubangijinsa, a kansa, ya ƙãra jin tsõro da tawãli'u.
"Kuma ƙirjĩna ya yi ƙunci* kuma harshẽna bã zai saku ba sabõda haka ka aika zuwa ga Harũna.
____________________
 * Mũsa yanã nũna cewa, shi yanã jin tsõro kada ya zama ya gajarta wajen iyar da manzanci, dõmin shi mai saurin fushine, yanã neman a taimake shi ɗan'uwansa Hãrũna.Wannan ya yi kama da farkon sũrar inda Annabi, tshĩra da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya nũna tsõron taƙaitãwa ga iyar da manzancin Allah zuwa ga mutãnensa dõmin haka ba su yi ĩmãni ba. Hãlin Annabawa duka ɗaya ne ga tsõron taƙaita aikin Ubangijinsu.
(Fir'auna) ya ce ga mashãwarta a gẽfensa, "Lalle ne, wannan haƙĩƙa, masihirci ne, mai ilmi!
Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shĩ da ɗan'uwansa, kuma ka aika mãsu gayya a cikin birãne."
Sai suka jẽfa igiyõyinsu, da sandunansu, kuma suka ce: "Da ƙarfin Fir'auna lalle ne mũ, haƙĩƙa, mũ ne marinjãya."
Verse 46
Sai aka jẽfar da masihirta sunã mãsu sujada.
Kuma Muka aika zuwa ga Mũsã cẽwa ka yi tafiyar dare da bãyiNa, lalle ne kũ waɗanda ake biyã* ne.
____________________
 * Mũsa yanã nũna cewa, shi yanã jin tsõro kada ya zama ya gajarta wajen iyar da manzanci, dõmin shi mai saurin fushine, yanã neman a taimake shi ɗan'uwansa Hãrũna.Wannan ya yi kama da farkon sũrar inda Annabi, tshĩra da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya nũna tsõron taƙaitãwa ga iyar da manzancin Allah zuwa ga mutãnensa dõmin haka ba su yi ĩmãni ba. Hãlin Annabawa duka ɗaya ne ga tsõron taƙaita aikin Ubangijinsu.
Verse 55
"Kuma lalle ne sũ, a gare Mu, Mãsu fusãtarwa ne."
Verse 56
"Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa gabã ɗaya mãsu sauna ne."
Verse 60
Sai suka bĩ su sunã mãsu fita a lõkacin hũdõwar rãnã.
Sa'an nan a lõkacin da jama'a biyu suka ga jũna, sai abõkan Mũsã suka ce: "Lalle ne mũ haƙĩ ƙa, waɗanda ake riska ne."
Sai Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã cẽwa "Ka dõki tẽku da sandarka." Sai tẽku ta tsãge,* kõwane tsãgi ya kasance kamar falalen dũtse mai girma.
____________________
 * Teku ta tsãge hanya gõma sha biyu a kan adadin danginBanĩ Isrãĩla. Suka bi suka wuce, sa'ilin nan aka nutsar daFir'auna, shi da jama'arsa, a cikin hanyõyin ruwan,.
Kuma Muka tsĩrar da Mũsã da waɗanda suke tãre da shi gabã ɗaya.
Verse 66
Sa'an nan kuma Muka nutsar da waɗansu mutãnen.
Kuma lalle ne Ubangijinka, kaƙĩƙa, Shĩ ne Mabũwayi, Mai jin ƙai.
Suka ce: "Munã bauta wa gumãka, sabõda haka munã yini mãsu lazimta a gare su."
Verse 79
"Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni."
"Kuma Ka sanya mini harshen gaskiya* a cikin mutãnen ƙarshe."
____________________
  * Harshen gaskiya shĩ ne yabõ mai kyau. Mutãnen ƙarshe sũ ne Musulmi al'ummar Annabi Muhammadu, mãsu shaida ga annabawa da iyar da manzanci
Verse 90
Kuma aka kusantar da Aljanna ga mãsu taƙawa.
Verse 91
Kuma aka fitar da wutã babba dõmin halakakku.
Verse 94
Sai aka kikkife su* a cikinta, su da halakakkun.
____________________
  * Gumãkan, sũ da halakakku mabiyansu. Dukkan mai ɓatarda wani shĩ ne gunki ga mai bin sa halakakke.
Verse 108
"To, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Verse 110
"Sabõda haka, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Suka ce: "Ashe, zã mu yi ĩmãni sabõda kai alhãli kuwa mafiya ƙasƙanci sun bi ka?"
Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, yã Nũhu, (daga maganarka,) haƙĩƙa, kanã kasancẽwa daga waɗanda ake jẽfewa"
"Sai ka yi hukunci, a tsakãnĩna da tsakãninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsĩrar da ni, da waɗanda suke tãre da ni daga mũminai."
Sai Muka tsĩrar da shi, shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lõdi.
Verse 122
Kuma Lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai Rahama.
Verse 125
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, haƙĩƙa, Manzo ne, amintacce."
Verse 126
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Verse 128
"Shin, kunã yin ginin sitadiyo* a kõwane tsauni ne, kunã yin wãsa?"
____________________
 * Sitãdiyo shi ne gidan wasanni da Turanci, alãmã da Lãrabci.
Verse 129
"Kuma kunã riƙon matsãrar ruwa, tsammãninku, ku dawwama?*"
____________________
* Kõ kuma wurãren sanã'õ'i kamar masãƙoƙi irin na zãmanin nan.
Verse 130
"Kuma idan kun yi damƙa, sai ku yi damƙar kunã mãsu tanƙwasãwa."
Verse 131
"To ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Verse 133
"Ya taimake ku da dabbõbin ni'ima da ɗiya."
Verse 137
"Wannan abu bai zamõ ba fãce hãlãyen* mutãnen farko."
____________________
 * Wãtau lãbarun mutãne waɗanda ba su ci gaba ba bã su son a yi rawa da nishãɗi. Anã karantawar ma'anar ƙaryar ta farko, watau wai tãtsũniya ce: a ce wai a hana ãyã akan tsaunuka dõmin wasanni. Suna nufi da ãya ko alãma gidãjen rawa da na nashãdi watau stadiyam da kasĩno. 
Verse 138
"Kuma mũ ba mu zama waɗanda ake yi wa azãba ba."
Verse 140
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
Verse 144
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã.
Verse 146
"Shin, anã barin ku* a cikin abin da yake a nan, kunã amintattu?"
____________________
* Kuna zaton zã a bar ku a irin wannan ni'ima' Allah bã zai karɓi rãyukanku ba kuma Ya yi muku hisãbi a kanta? Kayya! Zã a yi muku hisãbi a bãyan kun mutu an tsayar da ku, dõmin hisãbin ayyukan da kuka yi.
Verse 148
"Da shuke-shuke da dabĩ nai, 'ya'yan itãcensu hirtsi* mãsu narkẽwa a ciki?"
____________________
   * Hirtsi shi ne 'ya'yan itãce sãbabbi tun ba su nuna ba. Wãtau hirtsin gonakinsu idan an ci shi narkewã ya ke yi a cikin ciki, balle kuma 'ya'yan itãce nunannu.
Verse 150
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Ya ce: "Wannan rãkuma ce tanã da shan* yini, kuma kunã da shan yini sasanne."
____________________
* Kuna zaton zã a bar ku a irin wannan ni'ima' Allah bã zai karɓi rãyukanku ba kuma Ya yi muku hisãbi a kanta? Kayya! Zã a yi muku hisãbi a bãyan kun mutu an tsayar da ku, dõmin hisãbin ayyukan da kuka yi.
Verse 157
Sai suka sõke ta sa'an nan suka wãyi gari sunã mãsu nadãma.
A lõkacin da ɗan'uwansu,* Lũɗu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
____________________
  * Lũɗu ɗan'uwansu ne na zaman gari da aure kawai. Asalinsa ɗan baffan Ibrãhĩm ne, sun tãso daga gabas, ƙasar Bãbila suka yi hijira, har ibrahĩm ya sauka Habrũna a ƙasar Shãm, Lũɗu kuwa ya sauka a sadũm da alƙaryunta.
Verse 163
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Suka ce: "Lalle ne haƙĩƙa idan ba ka hanu ba, yã Lũɗu! Tĩlas ne kanã kasancẽwa daga waɗanda ake fitarwa (daga gari)."
Verse 169
"Ya Ubangijina! Ka tsĩrar da ni da iyãlĩna daga abin da suke aikatãwa."
Verse 170
Sabõda haka Muka tsĩrar da shi, Shi da mutãnensa gabã ɗaya.
Verse 175
Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
Verse 179
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa kuma ku yi mini ɗã'ã."
Verse 184
"Kuma ku ji tsõron Allah wanda Ya halitta ku, kũ da jama'ar farko."
Sai suka ƙaiyatã shi, sabõda haka, azãbar rãnar girgije* ta kãma su. Lalle ne ita, tã kasance azãbar yini mai girma.
____________________
 * An ruwaito cewa Allah Ya bũɗe musu ƙõfar Jahannama, zãfi ya hana su zama akõ'ina cikin gidãjensu, sa'an nan aka sanya girgije ya yi musu inuwa mai sanyi-sanyi har suka tãru a ciki, sa'an nan aka sanya girgijen ya kãma da wuta a kansu suka ƙõne kurmus kamar an gasa fãra. Suka kõma tõka kamar yadda suka nema daga Shu'aibu da a jefa musu ɓaɓɓake daga sama idan ya zama daga mãsu gaskiya.
Verse 192
Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne.
Verse 193
Rũhi* amintacce ne ya sauka da shi.
____________________
 * Rũhul Ƙudus, shi ne Jibirĩl, amincin Allah ya tabbata a gare shi.
Verse 196
Kuma lalle shin, haƙĩƙa, yanã a cikin litattafan (Manzannin) farko.
Verse 204
Ashe, to, da azãbarMu suke nẽman gaggãwa?
Verse 205
Ashe, to, kã gani, idan Muka jĩshe su daɗi a shẽkaru,
Verse 206
Sa'an nan abin da suka kasance anã yi musu wa'adi (da shi) ya jẽ musu,
Abin da suka kasance anã jĩshe su dãɗin bã zai tunkuɗe azãba ba daga gare* su.
____________________
   * Dã an bã su lõkaci mai tsawo sunã jin dãɗi da rãyuwar dũniya a cikinsa, to, rãnar da mutuwa kõ azãbar Allah ta je gare su, wannan lõkacin bã zai tunkuɗe mutuwar kõ azabar ba daga gare su.
Verse 210
Kuma (Alƙur'ãni) Shaiɗãnu ba su ɗõra sauka da shĩba.
Verse 211
Kuma bã ya kamãta a gare su (su Shaiɗãnu su sauka da shi), kuma ba su iyãwa.
Verse 212
Lalle ne sũ, daga saurãre, haƙĩƙa, waɗanda aka nĩsantar ne.
Sabõda haka, kada ka kira wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah, sai ka kasance daga waɗanda ake yi wa azãba.
Verse 214
Kuma ka yi gargaɗi ga danginka mafiya kusanci.
Kuma ka sassauta fikãfikanka* ga wanda ya bĩ ka daga mũminai.
____________________
  * Ka zama mai tausayi ga mũminai waɗanda suka bĩ ka, ka yi musu kamar yadda kãzã take yi wa 'ya'yanta ƙanana a lõkacin sanyi, kõ kuwa idan zã su yi barci dõmin ta kãre su daga cũta.
Sa'an nan idan suka sãɓã maka to ka ce: "Lalle nĩ, barrantacce ne daga abin da kuko aikatãwa."
Verse 220
Lalle Shi, Shi* ne Mai ji, Masani.
____________________
  * Allah Shi ne Mai ji, ji na gaskiya, kuma Masani, sani na gaskiya.
Shin, (kunã so) in gaya* muku a kan wanda Shaiɗãnnu kan sauka?
____________________
  * Wannan dõmin raddi ne gamãsu cewa aljannu ke gayawa Muhammadu, tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi, Alƙur'ãni. Aljannu bã su saukã sai ga maƙaryaci, mai zunubi' Muhammadu kuwa bã haka yake ba. Sabõda haka shi bã mahaukaci ba, kuma ba wanda aljannu suke gaya wa ba. Dukan abin da ya faɗa, to, wahayi ne daga Allah.
Verse 223
Sunã jẽfa (abin da suka) ji, alhãli kuwa mafi yawansu maƙaryata ne.
Verse 224
Kuma mawãƙa(5) halakakku ne ke bin su.
____________________
   (5) Siffõfin mawãƙa sun nũna cewa Annabi Muhammadu bã mawãƙi ba ne, dõmin bã shi da ɗaya daga cikin siffõfin mawãƙa. Kuma mabiyansa ba halakakku ba ne.
Shin, ba ku cẽwa, lalle ne sũ, cikin kõwane rango sunã yin ɗimuwa (su ƙẽtare haddi) ba?
تقدم القراءة