Fassarar Surar Abasa a الهوساوية daga الترجمة الهوساوية
Verse 1
ﭑﭒ
ﭓ
Yã game huska* kuma ya jũya bãya.
____________________
* Wani makãho, Abdullahi bin Ummi Maktũm ya je wurin Annabi dõmin ya musulunta, sai ya iske a lõkacin nan Annabi na ƙõƙarin shiryar da wasu manyan mutãne na Ƙuraishãwa, sai wannan makãhon ya yanke maganar Annabi da su, bã da saninsa ba, alhãli Annabi na bũrin su musulunta dõmin darajarsu ga idon mutãnensu. Saboda haka Annabi, (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), ya ɓata Fuska, ya tafi dõmin ɓacin ransa, saboda rashin musuluntarsu. Bãyan haka Annabi nã girmama Abdullahi ƙwarai, idan ya je wurinsa sai ya ce masa "Maraba da wanda Ubangijina Ya zarge ni sabõda shi." Kuma ya shimfiɗa masa mayafinsa, idan ya fita tafiya, yakan sanya shi riƙon garin Madina, ƙissar tana nũna girmamawar Allah ga Annabi da Ya ce: "Ya game Fuska." Bai ce masa: "Domin ka game Fuska" ba, sai ya faɗa a cikin hali mai sauƙi.".
____________________
* Wani makãho, Abdullahi bin Ummi Maktũm ya je wurin Annabi dõmin ya musulunta, sai ya iske a lõkacin nan Annabi na ƙõƙarin shiryar da wasu manyan mutãne na Ƙuraishãwa, sai wannan makãhon ya yanke maganar Annabi da su, bã da saninsa ba, alhãli Annabi na bũrin su musulunta dõmin darajarsu ga idon mutãnensu. Saboda haka Annabi, (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), ya ɓata Fuska, ya tafi dõmin ɓacin ransa, saboda rashin musuluntarsu. Bãyan haka Annabi nã girmama Abdullahi ƙwarai, idan ya je wurinsa sai ya ce masa "Maraba da wanda Ubangijina Ya zarge ni sabõda shi." Kuma ya shimfiɗa masa mayafinsa, idan ya fita tafiya, yakan sanya shi riƙon garin Madina, ƙissar tana nũna girmamawar Allah ga Annabi da Ya ce: "Ya game Fuska." Bai ce masa: "Domin ka game Fuska" ba, sai ya faɗa a cikin hali mai sauƙi.".
Verse 2
ﭔﭕﭖ
ﭗ
Sabõda makãho yã je masa.
Verse 3
ﭘﭙﭚﭛ
ﭜ
To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.
Verse 4
ﭝﭞﭟﭠ
ﭡ
Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?
Verse 5
ﭢﭣﭤ
ﭥ
Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.
Verse 6
ﭦﭧﭨ
ﭩ
Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!
Verse 7
ﭪﭫﭬﭭ
ﭮ
To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?
Verse 8
ﭯﭰﭱﭲ
ﭳ
Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.
Verse 9
ﭴﭵ
ﭶ
Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.
Verse 10
ﭷﭸﭹ
ﭺ
Kai kuma kã shagala ga barinsa!
Verse 11
ﭻﭼﭽ
ﭾ
A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.
Verse 12
ﭿﮀﮁ
ﮂ
Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).
Verse 13
ﮃﮄﮅ
ﮆ
(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,
Verse 14
ﮇﮈ
ﮉ
Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.
Verse 15
ﮊﮋ
ﮌ
A cikin hannãyen mala'iku marubũta.
Verse 16
ﮍﮎ
ﮏ
Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.
Verse 17
ﮐﮑﮒﮓ
ﮔ
An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!
Verse 18
ﮕﮖﮗﮘ
ﮙ
Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?
Verse 19
ﮚﮛﮜﮝ
ﮞ
Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).
Verse 20
ﮟﮠﮡ
ﮢ
Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.
Verse 21
ﮣﮤﮥ
ﮦ
Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.
Verse 22
ﮧﮨﮩﮪ
ﮫ
Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.
Verse 23
ﮬﮭﮮﮯﮰ
ﮱ
Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).
Verse 24
ﯓﯔﯕﯖ
ﯗ
To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.
Verse 25
ﯘﯙﯚﯛ
ﯜ
Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.
Verse 26
ﯝﯞﯟﯠ
ﯡ
Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.
Verse 27
ﯢﯣﯤ
ﯥ
Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.
Verse 28
ﯦﯧ
ﯨ
Da inabi da ciyãwa.
Verse 29
ﯩﯪ
ﯫ
Da zaitũni da itãcen dabĩno.
Verse 30
ﯬﯭ
ﯮ
Da lambuna, mãsu yawan itãce.
Verse 31
ﯯﯰ
ﯱ
Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.
Verse 32
ﯲﯳﯴ
ﯵ
Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.
Verse 33
ﯶﯷﯸ
ﯹ
To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.
Verse 34
ﯺﯻﯼﯽﯾ
ﯿ
Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.
Verse 35
ﰀﰁ
ﰂ
Da uwarsa da ubansa.
Verse 36
ﰃﰄ
ﰅ
Da mãtarsa da ɗiyansa.
Verse 37
ﰆﰇﰈﰉﰊﰋ
ﰌ
Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.
Verse 38
ﰍﰎﰏ
ﰐ
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.
Verse 39
ﰑﰒ
ﰓ
Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.
Verse 40
ﰔﰕﰖﰗ
ﰘ
Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.
Verse 41
ﭑﭒ
ﭓ
Baƙi zai rufe su.
Verse 42
ﭔﭕﭖﭗ
ﭘ
Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).
تقدم القراءة