سورة عبس

الترجمة الهوساوية

Fassarar Surar Abasa a الهوساوية daga الترجمة الهوساوية

الترجمة الهوساوية

الناشر

مجمع الملك فهد

Verse 1
Yã game huska* kuma ya jũya bãya.
____________________
  * Wani makãho, Abdullahi bin Ummi Maktũm ya je wurin Annabi dõmin ya musulunta, sai ya iske a lõkacin nan Annabi na ƙõƙarin shiryar da wasu manyan mutãne na Ƙuraishãwa, sai wannan makãhon ya yanke maganar Annabi da su, bã da saninsa ba, alhãli Annabi na bũrin su musulunta dõmin darajarsu ga idon mutãnensu. Saboda haka Annabi, (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), ya ɓata Fuska, ya tafi dõmin ɓacin ransa, saboda rashin musuluntarsu. Bãyan haka Annabi nã girmama Abdullahi ƙwarai, idan ya je wurinsa sai ya ce masa "Maraba da wanda Ubangijina Ya zarge ni sabõda shi." Kuma ya shimfiɗa masa mayafinsa, idan ya fita tafiya, yakan sanya shi riƙon garin Madina, ƙissar tana nũna girmamawar Allah ga Annabi da Ya ce: "Ya game Fuska." Bai ce masa: "Domin ka game Fuska" ba, sai ya faɗa a cikin hali mai sauƙi.".
Verse 3
To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.
Verse 6
Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!
Verse 9
Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.
Verse 13
(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,
Verse 14
Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.
Verse 15
A cikin hannãyen mala'iku marubũta.
Verse 16
Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.
Verse 19
Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).
Verse 20
Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.
Verse 21
Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.
Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).
Verse 31
Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.
تقدم القراءة