Fassarar Surar Al-Kiyama a الهوساوية daga الترجمة الهوساوية
Verse 1
ﮊﮋﮌﮍ
ﮎ
Bã sai Nã yi rantsuwa* da Rãnar ¡iyãma ba.
____________________
* Wasu na fassarawa: lna rantsuwa da Rãnar Ƙiyama. A ganina, da tabbatar da rantsuwar da kuma kore ta duka ɗaya ne, maƙasũdi dai jan hankalin mai karãtu ga abin da yake a ciki, na hikimar Allah.
____________________
* Wasu na fassarawa: lna rantsuwa da Rãnar Ƙiyama. A ganina, da tabbatar da rantsuwar da kuma kore ta duka ɗaya ne, maƙasũdi dai jan hankalin mai karãtu ga abin da yake a ciki, na hikimar Allah.
Verse 2
ﮏﮐﮑﮒ
ﮓ
Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin* kansa ba.
____________________
* Kowane rai na zargin kansa idan bai yi aikin alheri ba, ko kuma bai yi fiye da wanda ya yi ba, ko kuma bai aikata wanda ya fi kyãwo ba a lokacin aikinsa.
____________________
* Kowane rai na zargin kansa idan bai yi aikin alheri ba, ko kuma bai yi fiye da wanda ya yi ba, ko kuma bai aikata wanda ya fi kyãwo ba a lokacin aikinsa.
Verse 3
ﮔﮕﮖﮗﮘ
ﮙ
Sin, mutum yana zaton cẽwa bã zã Mu tãra ƙasusuwansa ba?
Verse 4
ﮚﮛﮜﮝﮞﮟ
ﮠ
Na'am! Mãsu ĩkon yi Muke a kan Mu daidaita gaɓõɓin yãtsunsa.
Verse 5
ﮡﮢﮣﮤﮥ
ﮦ
Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa.
Verse 6
ﮧﮨﮩﮪ
ﮫ
Yanã tambaya: "Yaushe ne Rãnar ¡iyãma?"
Verse 7
ﮬﮭﮮ
ﮯ
To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli).
Verse 8
ﮰﮱ
ﯓ
Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).
Verse 9
ﯔﯕﯖ
ﯗ
Aka tãra rãnã da watã
Verse 10
ﯘﯙﯚﯛﯜ
ﯝ
Mutum zai ce a rãn nan "Ina wurin gudu?"
Verse 11
ﯞﯟﯠ
ﯡ
A'aha! bãbu mafaka.
Verse 12
ﯢﯣﯤﯥ
ﯦ
zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a rãnar nan, yake.
Verse 13
ﯧﯨﯩﯪﯫﯬ
ﯭ
Ana gayã wa mutum, a rãnar nan, abin da ya gabatar da wanda ya jinkirtar.
Verse 14
ﯮﯯﯰﯱﯲ
ﯳ
Ba haka ba! Mutum, ga abin da ya shafi kansa, masani ne.
Verse 15
ﯴﯵﯶ
ﯷ
Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba).
Verse 16
ﯸﯹﯺﯻﯼﯽ
ﯾ
Kada ka mõtsar* da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi (Alƙur'ãni).
____________________
* Dangantakar wannan ãya da ta sama da ita, ita ce bambancin Annabi mai gaggawar karɓar umurnin Allah da ƙyamar kãfiri ga karɓarsa, da bayãnin sauƙaƙewar Allah ga mai bin umurninSa.
____________________
* Dangantakar wannan ãya da ta sama da ita, ita ce bambancin Annabi mai gaggawar karɓar umurnin Allah da ƙyamar kãfiri ga karɓarsa, da bayãnin sauƙaƙewar Allah ga mai bin umurninSa.
Verse 17
ﯿﰀﰁﰂ
ﰃ
Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa.
Verse 18
ﰄﰅﰆﰇ
ﰈ
To idan Muka karanta shi sai ka bi karatunsa.
Verse 19
ﰉﰊﰋﰌ
ﰍ
sa'an nan, lalle wãjibi ne a gare Mu, bayãninsa.
Verse 20
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
A'aha! Bã haka ba kunã son mai gaugawar nan (duniya) ne.
Verse 21
ﭖﭗ
ﭘ
Kunã barin ta ƙarshen (Lãhira).
Verse 22
ﭙﭚﭛ
ﭜ
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne.
Verse 23
ﭝﭞﭟ
ﭠ
Zuwa ga Ubangijinsu mãsu kallo ne.
Verse 24
ﭡﭢﭣ
ﭤ
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu gintsẽwa ne.
Verse 25
ﭥﭦﭧﭨﭩ
ﭪ
Sunã zaton a sako musu masĩfa mai karya tsatso.
Verse 26
ﭫﭬﭭﭮ
ﭯ
A'aha! Iadan (rai) ya kai ga karankarmai.
Verse 27
ﭰﭱﭲﭳ
ﭴ
kuma aka ce: "Wãne ne mai tawada?"
Verse 28
ﭵﭶﭷ
ﭸ
Kuma ya tabbata cẽwa rabuwa dai ce.
Verse 29
ﭹﭺﭻ
ﭼ
Kuma ƙwabri ya lauye da wani ƙwabri.
Verse 30
ﭽﭾﭿﮀ
ﮁ
Zuwa ga Ubangijinka, a rãnar nan, magargaɗa* take.
____________________
* Ranar kora mutane, kamar ana gargaɗa tumãki, zuwa ga tsayuwa a gaba ga Allah, dõmin hisabi.
____________________
* Ranar kora mutane, kamar ana gargaɗa tumãki, zuwa ga tsayuwa a gaba ga Allah, dõmin hisabi.
Verse 31
ﮂﮃﮄﮅ
ﮆ
To, bai gaskatã ba, kuma bai yi salla ba!
Verse 32
ﮇﮈﮉ
ﮊ
Amma dai ya ƙaryata, kuma ya jũya baya!
Verse 33
ﮋﮌﮍﮎﮏ
ﮐ
Sa'an nan, ya tafi zuwa ga mutãnensa, yana tãƙama.
Verse 34
ﮑﮒﮓ
ﮔ
Halaka tã tabbata a gare ka, sa'an nan ita ce mafi dãcewa.
Verse 35
ﮕﮖﮗﮘ
ﮙ
Sa'an nan, wata halaka tã tabbata a gare ka dõmin tã fi dãce wa.
Verse 36
ﮚﮛﮜﮝﮞ
ﮟ
Shin, mutum nã zaton a bar shi sagaga (wãto bãbu nufin kõme game da shi)?
Verse 37
ﮠﮡﮢﮣﮤﮥ
ﮦ
Bai kasance iɗgo na maniyyi ba, wanda ake jefarwa (a cikin mahaifa)
Verse 38
ﮧﮨﮩﮪﮫ
ﮬ
Sa'an nan, ya zama gudan jini, sa'an nan Allah Ya halitta shi, sa'an nan Ya daidaita gaɓõɓinsa;
Verse 39
ﮭﮮﮯﮰﮱ
ﯓ
Sa'an nan, Ya sanya daga gare shi, nau'i biyu: namiji damace?
Verse 40
Ashẽ wannan bai zama Mai iko ba bisa ga rãyar da matattu?*
____________________
* Ana son mai karãtu a nan ya ce: a ɓoye بلى وأنا على ذلك من الشاهدين.
____________________
* Ana son mai karãtu a nan ya ce: a ɓoye بلى وأنا على ذلك من الشاهدين.
تقدم القراءة