سورة القيامة

الترجمة الهوساوية

Fassarar Surar Al-Kiyama a الهوساوية daga الترجمة الهوساوية

الترجمة الهوساوية

الناشر

مجمع الملك فهد

Verse 1
Bã sai Nã yi rantsuwa* da Rãnar ¡iyãma ba.
____________________
* Wasu na fassarawa: lna rantsuwa da Rãnar Ƙiyama. A ganina, da tabbatar da rantsuwar da kuma kore ta duka ɗaya ne, maƙasũdi dai jan hankalin mai karãtu ga abin da yake a ciki, na hikimar Allah.
Verse 2
Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin* kansa ba.
____________________
* Kowane rai na zargin kansa idan bai yi aikin alheri ba, ko kuma bai yi fiye da wanda ya yi ba, ko kuma bai aikata wanda ya fi kyãwo ba a lokacin aikinsa.
Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa.
Verse 8
Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).
Verse 15
Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba).
Kada ka mõtsar* da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi (Alƙur'ãni).
____________________
 * Dangantakar wannan ãya da ta sama da ita, ita ce bambancin Annabi mai gaggawar karɓar umurnin Allah da ƙyamar kãfiri ga karɓarsa, da bayãnin sauƙaƙewar Allah ga mai bin umurninSa.
Verse 17
Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa.
Verse 20
A'aha! Bã haka ba kunã son mai gaugawar nan (duniya) ne.
Verse 21
Kunã barin ta ƙarshen (Lãhira).
Verse 24
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu gintsẽwa ne.
Verse 30
Zuwa ga Ubangijinka, a rãnar nan, magargaɗa* take.
____________________
 * Ranar kora mutane, kamar ana gargaɗa tumãki, zuwa ga tsayuwa a gaba ga Allah, dõmin hisabi.
Verse 34
Halaka tã tabbata a gare ka, sa'an nan ita ce mafi dãcewa.
Verse 35
Sa'an nan, wata halaka tã tabbata a gare ka dõmin tã fi dãce wa.
Shin, mutum nã zaton a bar shi sagaga (wãto bãbu nufin kõme game da shi)?
Sa'an nan, ya zama gudan jini, sa'an nan Allah Ya halitta shi, sa'an nan Ya daidaita gaɓõɓinsa;
Ashẽ wannan bai zama Mai iko ba bisa ga rãyar da matattu?*
____________________
 * Ana son mai karãtu a nan ya ce: a ɓoye بلى وأنا على ذلك من الشاهدين.
تقدم القراءة