Fassarar Surar Al-Mutaffifin a الهوساوية daga الترجمة الهوساوية
Verse 1
ﯖﯗ
ﯘ
Bone ya tabbata ga mãsu naƙƙasãwa.
Verse 2
ﯙﯚﯛﯜﯝﯞ
ﯟ
Waɗanda suke idan suka auna daga mutãne suna cika mũdu.
Verse 3
ﯠﯡﯢﯣﯤ
ﯥ
Kuma idan sun auna musu da zakka* ko da sikẽli, suna ragẽwa
____________________
* Mũdu.
____________________
* Mũdu.
Verse 4
ﯦﯧﯨﯩﯪ
ﯫ
Ashe! Waɗancan bã su tabbata cẽwa lalle sũ, ana tãyar da su ba?
Verse 5
ﭑﭒ
ﭓ
Domin yini mai girma.
Verse 6
ﭔﭕﭖﭗﭘ
ﭙ
Yinin da mutãne ke tãshi zuwa ga Ubangijin halitta?
Verse 7
ﭚﭛﭜﭝﭞﭟ
ﭠ
Haƙĩƙa lalle ne littãfin fãjirai dãhir, yana a cikin Sijjĩn.
Verse 8
ﭡﭢﭣﭤ
ﭥ
Kuma, mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽ wa Sijjĩn?
Verse 9
ﭦﭧ
ﭨ
Wani ittãfi ne rubũtacce.
Verse 10
ﭩﭪﭫ
ﭬ
Bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa.
Verse 11
ﭭﭮﭯﭰ
ﭱ
Waɗanda suke ƙaryatãwa game da rãnar sakamako.
Verse 12
Babũ mai ƙaryatãwa gare shi fãce dukan mai ƙẽtare haddi mai yawan zunubi.
Verse 13
Idan ana karãtun ãyõyinmu, a kansa, sai ya ce: tãtsũniyõyin mutãnen farko ne.
Verse 14
A'aha! Bã haka ba, abin da suka kasance suna aikatãwa dai, yã yi tsãtsa a cikin zukãtãnsu.
Verse 15
ﮍﮎﮏﮐﮑﮒ
ﮓ
A'aha! Haƙĩƙa, lalle ne sũ daga Ubangijinsu, rãnar nan, waɗanda ake shãmakancẽwa ne.
Verse 16
ﮔﮕﮖﮗ
ﮘ
Sa'an nan, lalle ne, sũ mãsu shiga cikin Jahĩm ne.
Verse 17
Sa'an nan a ce: "Wannan shi ne abin da kuka kasance kuna ƙaryatãwa game da shi."
Verse 18
ﮡﮢﮣﮤﮥﮦ
ﮧ
A'aha! Haƙĩƙa lalle ne littãfin mãsu ɗã'ã yana a cikin Illiyyĩna?
Verse 19
ﮨﮩﮪﮫ
ﮬ
Kuma mẽne ne yã sanar da kai abin da ake cẽwa Illiyyũna?
Verse 20
ﮭﮮ
ﮯ
Wani littãfi ne rubũtacce.
Verse 21
ﮰﮱ
ﯓ
Muƙarrabai* suke halarta shi.
____________________
* Malã'iku masu daraja.
____________________
* Malã'iku masu daraja.
Verse 22
ﯔﯕﯖﯗ
ﯘ
Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah tabbas suna cikin ni'ima.
Verse 23
ﯙﯚﯛ
ﯜ
A kan karagu, suna ta kallo.
Verse 24
ﯝﯞﯟﯠﯡ
ﯢ
Kana sani a cikin huskõkinsu, akwai kwarjinin ni'ima.
Verse 25
ﯣﯤﯥﯦ
ﯧ
Ana shãyar da sũ daga wata giya wadda aka yunƙe a kan rufinta.
Verse 26
¡arshen kurɓinta miski ne. To, a cikin wannan, mãsu gwagwarmaya su yi ta gwagwarmayar nẽma.
Verse 27
ﯰﯱﯲ
ﯳ
Kuma abin da ake gauraya ta da shi, daga tasnĩm yake.
Verse 28
ﯴﯵﯶﯷ
ﯸ
(Wato) wani marmaro ne wanda muƙarrabai ke sha daga gare shi.
Verse 29
Lalle ne, waɗanda suka kãfirta sun kasance (a dũniya) suna yi wa waɗanda suka yi ĩmãni dãriya.
Verse 30
ﰂﰃﰄﰅ
ﰆ
Kuma idan sun shuɗe su sai su dinga yin zunɗe.
Verse 31
ﰇﰈﰉﰊﰋﰌ
ﰍ
Kuma idan suka jũya zuwa ga iyãlansu, sai su tafi suna kãkãci.
Verse 32
ﰎﰏﰐﰑﰒﰓ
ﰔ
Kuma idan sun gan su sai su ce: "Lalle waɗannan ɓatattu ne."
Verse 33
ﰕﰖﰗﰘ
ﰙ
Alhãli kuwa, ba a aike su ba dõmin su zama mãsu tsaro a kansu.
Verse 34
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
To, yau fa (a Lãhira] waɗanda suka yi ĩmãni, sũ ke yi wa kãfirai dãriya.
Verse 35
ﭘﭙﭚ
ﭛ
A kan karagu, suna ta kallo.
Verse 36
ﭜﭝﭞﭟﭠﭡ
ﭢ
Shin an sãka ma kãfirai abin da suka kasance suna aikatawa?*
____________________
* Amsar tambaya "na'am.".
____________________
* Amsar tambaya "na'am.".
تقدم القراءة