Fassarar Surar Ar-Rahman a الهوساوية daga الترجمة الهوساوية
Verse 1
ﭷ
ﭸ
(Allah) Mai rahama.
Verse 2
ﭹﭺ
ﭻ
Yã sanar da Alƙur'ani.
Verse 3
ﭼﭽ
ﭾ
Yã halitta mutum.
Verse 4
ﭿﮀ
ﮁ
Yã sanar da shi bayãni (magana).
Verse 5
ﮂﮃﮄ
ﮅ
Rãnã da watã a kan lissãfi suke.
Verse 6
ﮆﮇﮈ
ﮉ
Kuma tsirrai mãsu yãɗo da itãce sunã tawãlu'i.
Verse 7
ﮊﮋﮌﮍ
ﮎ
Kuma samã Ya ɗaukaka ta, Kuma Yã aza sikẽli.
Verse 8
ﮏﮐﮑﮒ
ﮓ
Dõmin kada ku karkatar da sikẽlin.
Verse 9
ﮔﮕﮖﮗﮘﮙ
ﮚ
Kuma ku daidaita awo da ãdalci, kuma kada ku rage sikẽlin.
Verse 10
ﮛﮜﮝ
ﮞ
Kuma ƙasã Yã aza ta dõmin tãlikai.
Verse 11
ﮟﮠﮡﮢﮣ
ﮤ
A cikinta akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno mai kwasfa.
Verse 12
ﮥﮦﮧﮨ
ﮩ
Da ƙwãya mai sõshiya da ƙamshi.
Verse 13
ﮪﮫﮬﮭ
ﮮ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangjinku *kuke ƙaryatãwa?
____________________
* Asalin lamiri "ku" yanã nũni ne ga nau'i biyu, watau mutãne da aljannu, sai dai bãbu lamirin abu biyu kawai a cikin Hausa, sai na jama'a. Jam'i a luggar Hausa ya fara daga biyu.
____________________
* Asalin lamiri "ku" yanã nũni ne ga nau'i biyu, watau mutãne da aljannu, sai dai bãbu lamirin abu biyu kawai a cikin Hausa, sai na jama'a. Jam'i a luggar Hausa ya fara daga biyu.
Verse 14
ﮯﮰﮱﯓﯔ
ﯕ
Yã halitta mutum daga ƙẽkasasshen yumɓu kumar kasko.
Verse 15
ﯖﯗﯘﯙﯚﯛ
ﯜ
Kuma ya halitta aljani daga bira daga wutã.
Verse 16
ﯝﯞﯟﯠ
ﯡ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 17
ﯢﯣﯤﯥ
ﯦ
Ubangjin mafita biyu na rãnã, kuma Ubangijin mafãɗã biyu na rãnã.
Verse 18
ﯧﯨﯩﯪ
ﯫ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 19
ﭑﭒﭓ
ﭔ
Yã garwaya tẽku biyu (ruwan dãɗi da na zartsi) sunã haɗuwa.
Verse 20
ﭕﭖﭗﭘ
ﭙ
A tsakãninsu akwai shãmaki, bã za su ƙetare haddi ba.
Verse 21
ﭚﭛﭜﭝ
ﭞ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 22
ﭟﭠﭡﭢ
ﭣ
Lu'ulu'u da murjãni na fita daga gare su.
Verse 23
ﭤﭥﭦﭧ
ﭨ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 24
ﭩﭪﭫﭬﭭﭮ
ﭯ
Kuma Yanã da manyan jirãge, waɗanda ake ƙãgãwa a cikin tẽku kamar manyan duwãtsu.
Verse 25
ﭰﭱﭲﭳ
ﭴ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 26
ﭵﭶﭷﭸ
ﭹ
Dukkan wanda ke kanta* mai ƙãrẽwa ne.
____________________
* Yanã nufin ƙasa.
____________________
* Yanã nufin ƙasa.
Verse 27
ﭺﭻﭼﭽﭾﭿ
ﮀ
Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa.
Verse 28
ﮁﮂﮃﮄ
ﮅ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 29
wanda ke a cikin sammai da ƙasã yanã rõƙon Sa (Allah), a kullum Allah na a cikin wani sha'ani.
Verse 30
ﮒﮓﮔﮕ
ﮖ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 31
ﮗﮘﮙﮚ
ﮛ
Zã mu ɗauki lõkaci sabõda ku, yã kũ *mãsu nauyin halitta biyu!
____________________
* Mutãne da aljannu.
____________________
* Mutãne da aljannu.
Verse 32
ﮜﮝﮞﮟ
ﮠ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 33
Ya jama'ar aljannu da mutãne! Idan kunã iya zarcẽwa daga sãsannin sammai da ƙasã to ku zarce. Bã za ku iya zarcẽwaba fãce da wani dalĩli.
Verse 34
ﯔﯕﯖﯗ
ﯘ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 35
Anã sako wani harshe daga wata wutã a kanku, da narkakkiyar tagulla. To, bã zã ku nẽmi taimako ba?
Verse 36
ﯢﯣﯤﯥ
ﯦ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 37
ﯧﯨﯩﯪﯫﯬ
ﯭ
Sa'an nan idan sama ta tsãge kuma ta zama jã kamar jar fãta.
Verse 38
ﯮﯯﯰﯱ
ﯲ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 39
To, a ran nan bã zã a tambayi wani mutum laifinsa ba, kuma haka aljani.
Verse 40
ﯼﯽﯾﯿ
ﰀ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 41
ﰁﰂﰃﰄﰅﰆ
ﰇ
zã a iya sanin mãsu laifi da alãmarsu, sabõda haka sai a kãma kwarkaɗarsu da sãwãyensu.
Verse 42
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 43
ﭖﭗﭘﭙﭚﭛ
ﭜ
Wannan Jahannama ce wadda mãsu laifi ke ƙaryatãwa game da ita.
Verse 44
ﭝﭞﭟﭠﭡ
ﭢ
Sunã kẽwaya a tsakaninta da ruwan ɗimi mai tsananin tafasa.
Verse 45
ﭣﭤﭥﭦ
ﭧ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 46
ﭨﭩﭪﭫﭬ
ﭭ
Kuma wanda ya ji tsõron tsayãwa a gaba ga Ubangijinsa yanã da Aljanna biyu.
Verse 47
ﭮﭯﭰﭱ
ﭲ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 48
ﭳﭴ
ﭵ
Mãsu rassan itãce.
Verse 49
ﭶﭷﭸﭹ
ﭺ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 50
ﭻﭼﭽ
ﭾ
A cikinsu akwai marẽmari biyu sunã gudãna.
Verse 51
ﭿﮀﮁﮂ
ﮃ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 52
ﮄﮅﮆﮇﮈ
ﮉ
A cikinsu akwai nau'i biyu daga kõwane 'ya'yan itãcen marmari.
Verse 53
ﮊﮋﮌﮍ
ﮎ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 54
Sunã gincire a kan waɗansu shimfiɗu cikinsu tufãfin alharĩni mai kauri ne kuma nũnannun 'yã'yan itãcen Aljannar biyu kusakusa suke.
Verse 55
ﮚﮛﮜﮝ
ﮞ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 56
A cikinsu akwai mãtã mãsu taƙaita ganinsu, wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗebe budurcinsu ba kuma haka wani aljani.
Verse 57
ﮩﮪﮫﮬ
ﮭ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 58
ﮮﮯﮰ
ﮱ
Kamar dai su yaƙũtu ne da murjãni.
Verse 59
ﯓﯔﯕﯖ
ﯗ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 60
ﯘﯙﯚﯛﯜ
ﯝ
Shin, kyautatãwa nã da wani sakamako? (Ã'aha) fãce kyautatãwa.
Verse 61
ﯞﯟﯠﯡ
ﯢ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 62
ﯣﯤﯥ
ﯦ
Kuma baicinsu akwai waɗansu gidãjen Aljanna biyu.
Verse 63
ﯧﯨﯩﯪ
ﯫ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 64
ﯬ
ﯭ
Mãsu duhun inuwa.
Verse 65
ﯮﯯﯰﯱ
ﯲ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 66
ﯳﯴﯵ
ﯶ
A cikinsu akwai marẽmari biyu masu kwarãrar ruwa.
Verse 67
ﯷﯸﯹﯺ
ﯻ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 68
ﯼﯽﯾﯿ
ﰀ
A cikinsu akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno darummãni.
Verse 69
ﰁﰂﰃﰄ
ﰅ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 70
ﭑﭒﭓ
ﭔ
A cikinsu, akwai wasu mãtã mãsu kyaun hãlãye, mãsu kyaun halitta.
Verse 71
ﭕﭖﭗﭘ
ﭙ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 72
ﭚﭛﭜﭝ
ﭞ
Mãsu farin idãnu da baƙinsu waɗanda aka tsare a cikin haimõmi.
Verse 73
ﭟﭠﭡﭢ
ﭣ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 74
ﭤﭥﭦﭧﭨﭩ
ﭪ
Wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗẽbe budurcinsu ba, kuma haka wani aljani.
Verse 75
ﭫﭬﭭﭮ
ﭯ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 76
ﭰﭱﭲﭳﭴﭵ
ﭶ
Sunã gincire a kan wasu matãsai mãsu kõren launi da katĩfun Abkara kyãwãwa.
Verse 77
ﭷﭸﭹﭺ
ﭻ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Verse 78
ﭼﭽﭾﭿﮀﮁ
ﮂ
Sũnan Ubangjinka, Mai girman Jalãla da Karimci, ya tsarkaka.
تقدم القراءة