Fassarar Surar Ad-Dukhan a الهوساوية daga الترجمة الهوساوية
Verse 1
ﭑ
ﭒ
Ḥ. M̃.
Verse 2
ﭓﭔ
ﭕ
Inã rantsuwa da Littãfi Mabayyani.
Verse 3
Lalle ne, Mũ, Muka saukar da shi a cikin wani dare mai albarka. Lalle Mũ' Mun kasance Mãsu yin gargaɗi.
Verse 4
ﭠﭡﭢﭣﭤ
ﭥ
A cikinsa (shi daren) ake rarrabe kõwane umurui bayyananne.
Verse 5
Umurni na daga wurinMu. Lalle Mũ ne Muka kasanceMãsu aikãwã.
Verse 6
Sabõda rahama daga Ubangijinka. Lalle Shĩ, Shi ne Mai ji, Mãsani.
Verse 7
(Shĩ ne) Ubangijin sammai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu yaƙĩni (za ku gãne haka).
Verse 8
Babu abin bautãwa fãce Shi. Yana rãyarwa Kuma Yana kashẽwa. (Shi ne) Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko.
Verse 9
ﮍﮎﮏﮐﮑ
ﮒ
A'a sũ, sunã wãsã a cikin shakka.
Verse 10
ﮓﮔﮕﮖﮗﮘ
ﮙ
Sabõda haka, ka dakata rãnar da sama zã tã zo da hayãƙi bayyananne.
Verse 11
ﮚﮛﮜﮝﮞﮟ
ﮠ
Yanã rufe mutãne. Wannan wata azãba ce mai raɗaɗi.
Verse 12
ﮡﮢﮣﮤﮥﮦ
ﮧ
Ya Ubangijinmu! Ka kuranye mana azãba. Lalle Mũ, mãsu ĩmãni ne.
Verse 13
Inã tunãwa take a gare su, alhãli kuwa, haƙĩƙa, Manzo mai bayyanãwa Ya je musu (da gargaɗin saukar azãbar, ba su karɓa ba)?
Verse 14
ﮰﮱﯓﯔﯕﯖ
ﯗ
Sa'an nan suka jũya baya daga gare shi, Kuma suka ce: "Wanda ake gayãwa* ne, mahaukaci."
____________________
* Sunã nufin waɗansu mutãne ne ke gaya wa Annabi Alƙur'ãni, kõ kuma daga alãma watau wai Annabi taɓaɓɓe ne, mahaukaci. Taɓaɓɓe da mahaukaci duka ma'anarsu guda ce, watau marashin hankali,wanda aka yi wa alãma da rashin hankali.
____________________
* Sunã nufin waɗansu mutãne ne ke gaya wa Annabi Alƙur'ãni, kõ kuma daga alãma watau wai Annabi taɓaɓɓe ne, mahaukaci. Taɓaɓɓe da mahaukaci duka ma'anarsu guda ce, watau marashin hankali,wanda aka yi wa alãma da rashin hankali.
Verse 15
Lalle Mũ, Mãsu kuranyẽwar azãba ne, a ɗan lõkaci kaɗan, lalle kũ, mãsu kõmãwa ne (ga laifin).
Verse 16
ﯠﯡﯢﯣﯤﯥ
ﯦ
Rãnar da Muke damƙa, damƙa mafi girma, lalle ne Mũ mãsu azãbar rãmuwa ne.
Verse 17
Kuma lalle ne haƙĩƙa a gabaninsu, Mun fitini mutãnen Fir'auna, kuma wani Manzo karĩmi ya jẽ musu.
Verse 18
(Mazon ya ce): "Ku kãwo mini (ĩmãninku) ya bayin Allah! Lalle ni, Manzo ne amintacce zuwa gare ku."
Verse 19
"Kuma kada ku nẽmi ɗaukaka a kan Allah. Lalle nĩ mai zo muku ne da dalĩli bayyananne."
Verse 20
ﭜﭝﭞﭟﭠﭡ
ﭢ
"Kuma lalle nĩ na nẽmi tsari da Ubangijĩna, kuma Ubangijinku, dõmin kada ku jẽfe ni."
Verse 21
ﭣﭤﭥﭦﭧ
ﭨ
"Kuma idan ba ku yi ĩmãni sabõda nĩ ba, to, ku nĩsance ni."
Verse 22
ﭩﭪﭫﭬﭭﭮ
ﭯ
Sai ya kirayi Ubangjinsa cẽwa waɗannan mutãnene mãsu laifi.
Verse 23
ﭰﭱﭲﭳﭴ
ﭵ
(Allah Ya ce): "To, ka yi tafiyar dare da bayiNa, da dare. Lalle kũ, waɗanda ake bĩ ne (dõmin a kãma ku.)"
Verse 24
"Kuma ka bar tẽku rarrabe. Lalle sũ, runduna ce abar nutsarwa."
Verse 25
ﭾﭿﮀﮁﮂ
ﮃ
Da yawa suka bar gõnaki da marẽmari.
Verse 26
ﮄﮅﮆ
ﮇ
Da shuke-shuke da matsayi mai kyau.
Verse 27
ﮈﮉﮊﮋ
ﮌ
Da wata ni'ima da suka kasance a cikinta sunã mãsu hutu.
Verse 28
ﮍﮎﮏﮐﮑ
ﮒ
Kamar haka! Kuma Muka gãdar da ita ga waɗansu mutãne na dabam.
Verse 29
Sa'an nan samã da ƙasã ba su yi kũka *a kansu ba, Kuma ba su kasance waɗanda ake yi wa jinkiri ba.
____________________
* Watau sama da ƙasa ba su girgizu ba sabõda halaka su da aka yi kamar ba a yi, kõme ba.
____________________
* Watau sama da ƙasa ba su girgizu ba sabõda halaka su da aka yi kamar ba a yi, kõme ba.
Verse 30
Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun tsĩrar da Banĩ Isrã'ĩla daga, azãba mai wulãkantãwa.
Verse 31
Daga Fir'auna. Lalle shi, ya kasance maɗaukaki daga cikin mãsu ɓarna.
Verse 32
ﮭﮮﮯﮰﮱﯓ
ﯔ
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun zãɓe su sabõda wani ilmi (na Taurata) a kan mutãne.
Verse 33
Kuma Muka bã su, daga ãyõyin mu'ujizõji, abin da yake a cikinsa, akwai ni'ima bayyananna*
____________________
* An bai wa Banĩ lsrã'ĩla ni'imar ilmi na Taurãta, an ɗaukaka su, sabõda aiki da ilmin, a kan sauran mutãnen zãmaninsu, kuma aka bã su ãyõyin mu'ujiza kamar tsãge teku da mannu da salwa da sauransu, amma kuma dukkan waɗannan ni'imomĩn sai da suka gushe a lõkacin da suka sãɓawa umurnin Allah, sai kuma ƙasƙanci ya maye musu daga bãya. Wannan kuma wa'azi ne ga Musulmi waɗanda Allah Ya ɗaukaka su da Alƙur'ãni a kan sauran mutãne, idan sun kauce masa zã su wulãkantu.
____________________
* An bai wa Banĩ lsrã'ĩla ni'imar ilmi na Taurãta, an ɗaukaka su, sabõda aiki da ilmin, a kan sauran mutãnen zãmaninsu, kuma aka bã su ãyõyin mu'ujiza kamar tsãge teku da mannu da salwa da sauransu, amma kuma dukkan waɗannan ni'imomĩn sai da suka gushe a lõkacin da suka sãɓawa umurnin Allah, sai kuma ƙasƙanci ya maye musu daga bãya. Wannan kuma wa'azi ne ga Musulmi waɗanda Allah Ya ɗaukaka su da Alƙur'ãni a kan sauran mutãne, idan sun kauce masa zã su wulãkantu.
Verse 34
ﯝﯞﯟ
ﯠ
Lalle waɗannan mutãne*, haƙĩka, sunã cẽwa,
____________________
* Anã nufin mutãnen zãmanin Annabi Muhammadu, tsĩra da aminci su tabbata a gare shi, waɗanda ake kiran su zuwa ga Musulunci.
____________________
* Anã nufin mutãnen zãmanin Annabi Muhammadu, tsĩra da aminci su tabbata a gare shi, waɗanda ake kiran su zuwa ga Musulunci.
Verse 35
"Babu wani abu sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake tãyarwa ba."
Verse 36
ﯪﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
"Sai ku zo da ubanninmu, idan kun kasance mãsu gaskiya."
Verse 37
shin, sũ ne mafĩfĩta kõ kuwa mutãnen Tubba'u, kuma da waɗanda ke a gabãninsu? Mun halaka su, lalle sũ, sun kasance mãsu laifi.
Verse 38
Kuma ba Mu halitta slmmai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu ba, alhãli kuwa Munã mãsu wãsã.
Verse 39
Ba Mu halitta su ba fãce da manufa ta gaskiya, kuma amma mafi yawansu, ba su sani ba.
Verse 40
ﭑﭒﭓﭔﭕ
ﭖ
Lalle rãnar rarrabẽwa, ita ce lõkacin wa'adinsu gabã ɗaya.
Verse 41
Rãnar da wani zumu bã ya amfãnin wani zumu da kõme kuma ba su zama anã taimakon su ba.
Verse 42
fãce wanda Allah Ya yi wa rahama. Lalle Shi (Allah), shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
Verse 43
ﭫﭬﭭ
ﭮ
Lalle itãciyar zaƙƙũm (ɗanyen wutã),
Verse 44
ﭯﭰ
ﭱ
Ita ce abincin mai laifi.
Verse 45
ﭲﭳﭴﭵ
ﭶ
Kamar narkakken kwalta yanã tafasa a cikin cikunna.
Verse 46
ﭷﭸ
ﭹ
Kamar tafasar ruwan zãfi.
Verse 47
ﭺﭻﭼﭽﭾ
ﭿ
(A cẽ wa malã'ikun wutã), "Ku kãmã shi, sa'an nan ku fizge shi zuwa ga tsakiyar Jahĩm."
Verse 48
"Sa'an nan ku zuba, a kansa, daga azãbar ruwan zãfi."
Verse 49
ﮈﮉﮊﮋﮌ
ﮍ
(A ce masã), "Ka ɗanɗana! Lalle kai, kai ne mabuwãyi mai girma!"
Verse 50
ﮎﮏﮐﮑﮒﮓ
ﮔ
"Lalle wannan, shi ne abin da kuka kasance kunã shakka game da shi."
Verse 51
ﮕﮖﮗﮘﮙ
ﮚ
Lalle mãsu taƙawa sunã cikin matsayi amintacce.
Verse 52
ﮛﮜﮝ
ﮞ
A cikin gidãjen Aljanna da marẽmari.
Verse 53
ﮟﮠﮡﮢﮣ
ﮤ
Sunã tufanta daga tufãfin alharĩni raƙĩƙi, da mai kauri, sunã mãsu zaman fuskantar jũna.
Verse 54
ﮥﮦﮧﮨ
ﮩ
Kamar haka, kuma Mun aurar da su da mãtã mãsu kyaun idãnu, mãsu girmansu.
Verse 55
ﮪﮫﮬﮭﮮ
ﮯ
Sunã kira, a cikinsu (gidẽjen) ga dukan 'ya'yan itãcen marmari, sunã amintattu (daga dukan abin tsõro).
Verse 56
Bã su ɗanɗanar mutuwa, a cikinsu, fãce mutuwar farko, kuma (Allah), Ya tsare musu azãbar Jahĩm.
Verse 57
Sabõda falala daga Ubangijinka. Wancan shi ne babban rabo, mai girma.
Verse 58
ﯦﯧﯨﯩﯪ
ﯫ
Dõmin haka kawai Muka sauƙaƙar da shi (Alƙur'ãni) da harshenka, tsammãninsu, su riƙa tunãwa.
Verse 59
ﯬﯭﯮ
ﯯ
Sai ka yi jira. Lalle sũ, mãsu jira ne.*
____________________
* Mãsu jira ne ga abin da zai sãme su idan ba su yi ĩmãni ba, watau ni'imar da aka ba su zã ta gushe ke nan dõmin ba su aiwatar da ita ba a kan umuruin Allah.
____________________
* Mãsu jira ne ga abin da zai sãme su idan ba su yi ĩmãni ba, watau ni'imar da aka ba su zã ta gushe ke nan dõmin ba su aiwatar da ita ba a kan umuruin Allah.
تقدم القراءة