سورة النجم

الترجمة الهوساوية

Fassarar Surar An-Najm a الهوساوية daga الترجمة الهوساوية

الترجمة الهوساوية

الناشر

مجمع الملك فهد

Verse 1
Inã rantsuwa da taurãron, a lõkacin da ya faku.
Verse 5
(Malã'ika) mai tsananin ƙarfi *ya sanar da shi.
____________________
* Wahayin da ke zuwa ga Annabi bãbu ɓata a cikinsa dõmin Jibrilu mai kãwo shi ga Annabi, Malã'ika ne mai ƙarfi ƙwarai, wani Shaiɗãni bã ya iya taron sa dõmin ya musanya wahayin, kuma Annabi ya san shi sõsai, kuma idan ya kãwo wahayin, sai ya sauko kusa ƙwarai da Annabi, sa'an nan shi kuma Annabi ba rikitacce ba ne, yanã cikin hankalinsa.
Verse 6
Ma'abũcin ƙarfi da kwarjini, sa'an nan ya daidaita.
Verse 7
Alhãli kuwa yanã a sararin samã mafi aukaka.
Sa'an nan ya yi wahayi zuwa ga bãwan Allah (Muhammadu) da abin da ya faɗa (masa).
Verse 13
Kuma lalle ya gan shi, haƙĩƙatan, a wani lõkacin saukarsa.*
____________________
* Lamirin Malã'ika Jibrila ne.
Ganinsa* bai karkata ba, kuma bai ƙetare haddi ba.
____________________
* Lamirin Malã'ika Jibrila ne.
Lalle, tabbas, (Annabinku) ya ga waɗanda suka fi girma* daga ãyõyin Ubangijinsa.
____________________
 * Watau dai Alƙur'ani ya zo daga Allah ta hanya mafi aminci har ya sadu da mutãne dõmin su yi aiki da abin da ke cikinsa.
Verse 19
Shin, kun ga Lãta da uzza?(5)
____________________
 (5) Watau kun bar Alƙur'ani kun kõma wa surkullen da kuke haɗãwa game da gumãka su Lãta da Uzza da Manãta. Kuna cewa sũ wakĩlan Mala'ikun da kuke bautã wa ne kuma su 'ya'yan Allah mãtã ne. Sunã cetonku daga Allah.
Verse 21
Ashe, kũ ne da ɗa namiji Shĩ (Allah) kuma da ɗiya mace?
Waɗannan bã kõme ba ne fãce sũnãye, waɗanda kuka ambace su da su, kũ da uwãyenku. Allah bai saukar da wani dalĩli game da su ba. (Kãfirai) bã su biyar kõme fãce zato da abin da rãyukansu ke so, Alhãli kuwa shiriyar(6) ta daga wajen Ubangijinsu, ta jẽ musu (sai suka bar ta suka kõma wa zaton).
____________________
(6) Watau Alƙur'ani wanda Mala'ika jibrĩla ya zo wa Annabi da shi. Sun bar shi sun kõma wa tatsũniyõyi da gũrace-gũrace.
Verse 25
To, Lãhira da dũniya na Allah kawai ne (wanda ya nẽme su daga wani, yã yi kuskure).
Kuma abin da ke cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasã na Allah kawai ne, dõmin Yã sãka wa waɗanda suka mũnana da abin da suka aikata, kuma Ya sãka wa waɗanda suki kyautata da sakamakon da ya fi kyau.
Waɗanda ke nĩsantar manyan zunubai da abũbuwan alfãsha, fãce ƙanãnan laifuffuka, lalle Ubangijinka Mai yalwatattar gãfara ne, Shĩ ne Ya fi sani ga abinda ke gare ku a lõkacin da Ya ƙãga halittarku daga ƙasa, kuma a lõkacin da kuke tãyuna a cikin cikannan uwãyenku. Sabõda haka, kada ku tsarkake* kanku, Shĩ ne Mafi sani ga wanda ya yi taƙawa.
____________________
  * Wanda yake mutumin kirki, Allah Ya san shi. Kada ku dinga tsarkake kanku da bãkunanku dõmin neman girma, kõ dõmin neman wani abu dabam.
Verse 41
Sa'an nan a sãka masa da sakamako wanda yake mafi cikar ma'auni?
Verse 43
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya sanya dariya, kuma Ya sanya kũka.
Verse 46
Daga wani ɗigon ruwa guda a lõkacin da ake jẽfa shi a cikin mahaifa.
Verse 49
Kuma lalle, Shĩ, Shi ne Ubangijin Shi'ira.*
____________________
* Sũnan wasu taurãri biyu ne sunã fita a bãyan taurarin Jauza'a sunã tafiya daga kudu zuwa arewa karkace. Kabĩlar Lãrabãwa ta Khuza'a na bauta musu da umurnin Abu Kabshah, ɗaya daga cikin kãkannin Annabi na wajen uwa dõmin haka ne Ƙuraishãwa ke ce wa Annabi Ibn abĩ Kabshah, wanda ya ƙãga sãbon addinĩn da ya sãɓawa na ubanninsa.
Verse 53
Da waɗanda aka birkice *ƙasarsu, Ya kãyar da su.
____________________
 * Mutãnen Lũɗu da aka birkice ƙasarsu da su.
Verse 55
To, da wace daga ni'imõmin Ubangijinka kake *yin shakka?
____________________
* Kamar abõkin magana kõ mai karãtu.
wannan (Muhammadu) mai gargaɗi ne kamar irin mãsu gargaɗi na farko.
Verse 57
Makusanciya* fa, tã yi kusa.
____________________
 * Makusanciya ita ce Ƙiyãma.
Verse 59
Shin, kuma daga wannan (5)lãbãri kuke mãmãki?
____________________
 (5) Al'ƙur'ãni.
Verse 60
Kuma kunã yin dãriya, kuma bã ku yin kũka?
Verse 62
To, ku yi tawãli'u (6)ga Allah, kuma ku bauta (masa).
____________________
 (6) Anã yin sujadar karatu a nan, amma bã ta a cikin sujadai na tĩlas.
تقدم القراءة