Fassarar Surar An-Najm a الهوساوية daga الترجمة الهوساوية
Verse 1
ﭑﭒﭓ
ﭔ
Inã rantsuwa da taurãron, a lõkacin da ya faku.
Verse 2
ﭕﭖﭗﭘﭙ
ﭚ
Ma'abũcinku bai ɓata ba, kuma bai ƙẽtare haddi ba.
Verse 3
ﭛﭜﭝﭞ
ﭟ
Kuma bã ya yin magana daga son zuciyarsa.
Verse 4
ﭠﭡﭢﭣﭤ
ﭥ
(Maganarsa) ba ta zamo ba, fãce wahayi ne da ake aikõwa.
Verse 5
ﭦﭧﭨ
ﭩ
(Malã'ika) mai tsananin ƙarfi *ya sanar da shi.
____________________
* Wahayin da ke zuwa ga Annabi bãbu ɓata a cikinsa dõmin Jibrilu mai kãwo shi ga Annabi, Malã'ika ne mai ƙarfi ƙwarai, wani Shaiɗãni bã ya iya taron sa dõmin ya musanya wahayin, kuma Annabi ya san shi sõsai, kuma idan ya kãwo wahayin, sai ya sauko kusa ƙwarai da Annabi, sa'an nan shi kuma Annabi ba rikitacce ba ne, yanã cikin hankalinsa.
____________________
* Wahayin da ke zuwa ga Annabi bãbu ɓata a cikinsa dõmin Jibrilu mai kãwo shi ga Annabi, Malã'ika ne mai ƙarfi ƙwarai, wani Shaiɗãni bã ya iya taron sa dõmin ya musanya wahayin, kuma Annabi ya san shi sõsai, kuma idan ya kãwo wahayin, sai ya sauko kusa ƙwarai da Annabi, sa'an nan shi kuma Annabi ba rikitacce ba ne, yanã cikin hankalinsa.
Verse 6
ﭪﭫﭬ
ﭭ
Ma'abũcin ƙarfi da kwarjini, sa'an nan ya daidaita.
Verse 7
ﭮﭯﭰ
ﭱ
Alhãli kuwa yanã a sararin samã mafi aukaka.
Verse 8
ﭲﭳﭴ
ﭵ
Sa'an nan ya kusanta, kuma ya matsa zurõwa.
Verse 9
ﭶﭷﭸﭹﭺ
ﭻ
Har ya kasance gwargwadon zirã'i biyu, kõ kuma abin da ya fi kusa.
Verse 10
ﭼﭽﭾﭿﮀ
ﮁ
Sa'an nan ya yi wahayi zuwa ga bãwan Allah (Muhammadu) da abin da ya faɗa (masa).
Verse 11
ﮂﮃﮄﮅﮆ
ﮇ
Zũciyar (Annabi) bata ƙaryata abin da ya gani ba.
Verse 12
ﮈﮉﮊﮋ
ﮌ
Shin, zã ku yi masa musu a kan abin da yake gani?
Verse 13
ﮍﮎﮏﮐ
ﮑ
Kuma lalle ya gan shi, haƙĩƙatan, a wani lõkacin saukarsa.*
____________________
* Lamirin Malã'ika Jibrila ne.
____________________
* Lamirin Malã'ika Jibrila ne.
Verse 14
ﮒﮓﮔ
ﮕ
A wurin da magaryar tuƙẽwa take.
Verse 15
ﮖﮗﮘ
ﮙ
A inda taken, nan Aljannar makoma take.
Verse 16
ﮚﮛﮜﮝﮞ
ﮟ
Lõkacin da abin da yake rufe magaryar tuƙẽwa ya rufe ta.
Verse 17
ﮠﮡﮢﮣﮤ
ﮥ
Ganinsa* bai karkata ba, kuma bai ƙetare haddi ba.
____________________
* Lamirin Malã'ika Jibrila ne.
____________________
* Lamirin Malã'ika Jibrila ne.
Verse 18
ﮦﮧﮨﮩﮪﮫ
ﮬ
Lalle, tabbas, (Annabinku) ya ga waɗanda suka fi girma* daga ãyõyin Ubangijinsa.
____________________
* Watau dai Alƙur'ani ya zo daga Allah ta hanya mafi aminci har ya sadu da mutãne dõmin su yi aiki da abin da ke cikinsa.
____________________
* Watau dai Alƙur'ani ya zo daga Allah ta hanya mafi aminci har ya sadu da mutãne dõmin su yi aiki da abin da ke cikinsa.
Verse 19
ﮭﮮﮯ
ﮰ
Shin, kun ga Lãta da uzza?(5)
____________________
(5) Watau kun bar Alƙur'ani kun kõma wa surkullen da kuke haɗãwa game da gumãka su Lãta da Uzza da Manãta. Kuna cewa sũ wakĩlan Mala'ikun da kuke bautã wa ne kuma su 'ya'yan Allah mãtã ne. Sunã cetonku daga Allah.
____________________
(5) Watau kun bar Alƙur'ani kun kõma wa surkullen da kuke haɗãwa game da gumãka su Lãta da Uzza da Manãta. Kuna cewa sũ wakĩlan Mala'ikun da kuke bautã wa ne kuma su 'ya'yan Allah mãtã ne. Sunã cetonku daga Allah.
Verse 20
ﮱﯓﯔ
ﯕ
Da (wani gunki wai shi) Manãta, na ukunsu?
Verse 21
ﯖﯗﯘﯙ
ﯚ
Ashe, kũ ne da ɗa namiji Shĩ (Allah) kuma da ɗiya mace?
Verse 22
ﯛﯜﯝﯞ
ﯟ
Wannan fa ya zama rabo naƙasasshe.
Verse 23
Waɗannan bã kõme ba ne fãce sũnãye, waɗanda kuka ambace su da su, kũ da uwãyenku. Allah bai saukar da wani dalĩli game da su ba. (Kãfirai) bã su biyar kõme fãce zato da abin da rãyukansu ke so, Alhãli kuwa shiriyar(6) ta daga wajen Ubangijinsu, ta jẽ musu (sai suka bar ta suka kõma wa zaton).
____________________
(6) Watau Alƙur'ani wanda Mala'ika jibrĩla ya zo wa Annabi da shi. Sun bar shi sun kõma wa tatsũniyõyi da gũrace-gũrace.
____________________
(6) Watau Alƙur'ani wanda Mala'ika jibrĩla ya zo wa Annabi da shi. Sun bar shi sun kõma wa tatsũniyõyi da gũrace-gũrace.
Verse 24
ﯼﯽﯾﯿ
ﰀ
Ko (an fai cẽwa) mutum zai sãmi abin da yake gũri?
Verse 25
ﰁﰂﰃ
ﰄ
To, Lãhira da dũniya na Allah kawai ne (wanda ya nẽme su daga wani, yã yi kuskure).
Verse 26
Akwai malã'iku da yawa a cikin sammai cẽtonsu bã ya wadãtar da kõme fãce bãyan Allah Yã yi izni (da shi) ga wanda Yake so, kuma Yake yarda.
Verse 27
Lalle waɗannan da bã su yin ĩmãni da Lãhira, haƙĩƙa sunã kiran malã'iku da sũnan mace.
Verse 28
Kuma bã su da wani ilmi game da shi, bã su bin kõme fãce zato alhãli kuwa lalle zato bã ya amfãnar da kõme daga gaskiya.
Verse 29
Sabõda haka sai ka kau da kai daga wanda ya jũya bãya daga ambatonMu kuma bai yi nufin kõme ba fãce rãyuwar kusa (dũniya).
Verse 30
Wannan ita ce iyãkar abin da suke iya kai gare shi na ilmi. lalle Ubangijinka Shĩ ne Mafi sanin wanda ya ɓace daga hanyarSa, kuma Shi ne Mafi sani ga wanda ya nẽmi shiriya.
Verse 31
Kuma abin da ke cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasã na Allah kawai ne, dõmin Yã sãka wa waɗanda suka mũnana da abin da suka aikata, kuma Ya sãka wa waɗanda suki kyautata da sakamakon da ya fi kyau.
Verse 32
Waɗanda ke nĩsantar manyan zunubai da abũbuwan alfãsha, fãce ƙanãnan laifuffuka, lalle Ubangijinka Mai yalwatattar gãfara ne, Shĩ ne Ya fi sani ga abinda ke gare ku a lõkacin da Ya ƙãga halittarku daga ƙasa, kuma a lõkacin da kuke tãyuna a cikin cikannan uwãyenku. Sabõda haka, kada ku tsarkake* kanku, Shĩ ne Mafi sani ga wanda ya yi taƙawa.
____________________
* Wanda yake mutumin kirki, Allah Ya san shi. Kada ku dinga tsarkake kanku da bãkunanku dõmin neman girma, kõ dõmin neman wani abu dabam.
____________________
* Wanda yake mutumin kirki, Allah Ya san shi. Kada ku dinga tsarkake kanku da bãkunanku dõmin neman girma, kõ dõmin neman wani abu dabam.
Verse 33
ﯢﯣﯤ
ﯥ
Shin, ka ga wannan da ya jũya baya?
Verse 34
ﯦﯧﯨ
ﯩ
Ya yi kyauta kaɗan, kuma ya yi rowa?
Verse 35
ﯪﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
Shin, akwai ilmin gaibi a wurinsa, Sabõda haka yanã ganin gaibin?
Verse 36
Ko kuwa ba a ba shi lãbãri ba ga abin da yake a cikin Littafan Mũsã?
Verse 37
ﯸﯹﯺ
ﯻ
Da Ibrãhĩm wanda ya cika alkawari?
Verse 38
ﯼﯽﯾﯿﰀ
ﰁ
Cẽwa wani rai mai kãyan laifi bã ya ɗaukar kãyan laifin wani.
Verse 39
ﰂﰃﰄﰅﰆﰇ
ﰈ
Kuma mutum bã shi da kõme fãce abin da ya aikata.
Verse 40
ﰉﰊﰋﰌ
ﰍ
Kuma lalle, aikinsa zã a gan shi.
Verse 41
ﰎﰏﰐﰑ
ﰒ
Sa'an nan a sãka masa da sakamako wanda yake mafi cikar ma'auni?
Verse 42
ﰓﰔﰕﰖ
ﰗ
Kuma lalle, makõmar zuwa Ubangijinka kawai take?
Verse 43
ﰘﰙﰚﰛ
ﰜ
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya sanya dariya, kuma Ya sanya kũka.
Verse 44
ﰝﰞﰟﰠ
ﰡ
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya kashe, kuma Ya rãyar.
Verse 45
ﭑﭒﭓﭔﭕ
ﭖ
Kuma lalle Shĩ ne Ya yi halitta nau'i-nau'i, namiji da mace.
Verse 46
ﭗﭘﭙﭚ
ﭛ
Daga wani ɗigon ruwa guda a lõkacin da ake jẽfa shi a cikin mahaifa.
Verse 47
ﭜﭝﭞﭟ
ﭠ
Kuma a kansa ne ƙãga halitta ta biyu take.
Verse 48
ﭡﭢﭣﭤ
ﭥ
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya azurta, kuma Ya wadãtar.
Verse 49
ﭦﭧﭨﭩ
ﭪ
Kuma lalle, Shĩ, Shi ne Ubangijin Shi'ira.*
____________________
* Sũnan wasu taurãri biyu ne sunã fita a bãyan taurarin Jauza'a sunã tafiya daga kudu zuwa arewa karkace. Kabĩlar Lãrabãwa ta Khuza'a na bauta musu da umurnin Abu Kabshah, ɗaya daga cikin kãkannin Annabi na wajen uwa dõmin haka ne Ƙuraishãwa ke ce wa Annabi Ibn abĩ Kabshah, wanda ya ƙãga sãbon addinĩn da ya sãɓawa na ubanninsa.
____________________
* Sũnan wasu taurãri biyu ne sunã fita a bãyan taurarin Jauza'a sunã tafiya daga kudu zuwa arewa karkace. Kabĩlar Lãrabãwa ta Khuza'a na bauta musu da umurnin Abu Kabshah, ɗaya daga cikin kãkannin Annabi na wajen uwa dõmin haka ne Ƙuraishãwa ke ce wa Annabi Ibn abĩ Kabshah, wanda ya ƙãga sãbon addinĩn da ya sãɓawa na ubanninsa.
Verse 50
ﭫﭬﭭﭮ
ﭯ
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya halaka Ãdãwa na farko.
Verse 51
ﭰﭱﭲ
ﭳ
Da Samũdãwa, sa'an nan bai rage su ba.
Verse 52
Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sũ sun kasance mafi zãlunci kuma mafi girman kai.
Verse 53
ﭿﮀ
ﮁ
Da waɗanda aka birkice *ƙasarsu, Ya kãyar da su.
____________________
* Mutãnen Lũɗu da aka birkice ƙasarsu da su.
____________________
* Mutãnen Lũɗu da aka birkice ƙasarsu da su.
Verse 54
ﮂﮃﮄ
ﮅ
Sa'an nan abin da ya rufe su, ya rufe su.
Verse 55
ﮆﮇﮈﮉ
ﮊ
To, da wace daga ni'imõmin Ubangijinka kake *yin shakka?
____________________
* Kamar abõkin magana kõ mai karãtu.
____________________
* Kamar abõkin magana kõ mai karãtu.
Verse 56
ﮋﮌﮍﮎﮏ
ﮐ
wannan (Muhammadu) mai gargaɗi ne kamar irin mãsu gargaɗi na farko.
Verse 57
ﮑﮒ
ﮓ
Makusanciya* fa, tã yi kusa.
____________________
* Makusanciya ita ce Ƙiyãma.
____________________
* Makusanciya ita ce Ƙiyãma.
Verse 58
ﮔﮕﮖﮗﮘﮙ
ﮚ
Bãbu wani rai, banda Allah, mai iya bãyani gare ta.
Verse 59
ﮛﮜﮝﮞ
ﮟ
Shin, kuma daga wannan (5)lãbãri kuke mãmãki?
____________________
(5) Al'ƙur'ãni.
____________________
(5) Al'ƙur'ãni.
Verse 60
ﮠﮡﮢ
ﮣ
Kuma kunã yin dãriya, kuma bã ku yin kũka?
Verse 61
ﮤﮥ
ﮦ
Alhãli kunã mãsu wãsã?
Verse 62
ﮧﮨﮩﮪ
ﮫ
To, ku yi tawãli'u (6)ga Allah, kuma ku bauta (masa).
____________________
(6) Anã yin sujadar karatu a nan, amma bã ta a cikin sujadai na tĩlas.
____________________
(6) Anã yin sujadar karatu a nan, amma bã ta a cikin sujadai na tĩlas.
تقدم القراءة