Fassarar Surar An-Najm a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
Verse 1
ﭑﭒﭓ
ﭔ
An-Najm
Inã rantsuwa da taurãron, a lõkacin da ya faku.
Verse 2
ﭕﭖﭗﭘﭙ
ﭚ
Ma'abũcinku bai ɓata ba, kuma bai ƙẽtare haddi ba.
Verse 3
ﭛﭜﭝﭞ
ﭟ
Kuma bã ya yin magana daga son zuciyarsa.
Verse 4
ﭠﭡﭢﭣﭤ
ﭥ
(Maganarsa) ba ta zamo ba, fãce wahayi ne da ake aikõwa.
Verse 5
ﭦﭧﭨ
ﭩ
(Malã'ika) mai tsananin ƙarfi ya sanar da shi.
Verse 6
ﭪﭫﭬ
ﭭ
Ma'abũcin ƙarfi da kwarjini, sa'an nan ya daidaita.
Verse 7
ﭮﭯﭰ
ﭱ
Alhãli kuwa yanã a sararin samã mafi aukaka.
Verse 8
ﭲﭳﭴ
ﭵ
Sa'an nan ya kusanta, kuma ya matsa zurõwa.
Verse 9
ﭶﭷﭸﭹﭺ
ﭻ
Har ya kasance gwargwadon zirã'i biyu, kõ kuma abin da ya fi kusa.
Verse 10
ﭼﭽﭾﭿﮀ
ﮁ
Sa'an nan ya yi wahayi zuwa ga bãwan Allah (Muhammadu) da abin da ya faɗa (masa).
Verse 11
ﮂﮃﮄﮅﮆ
ﮇ
Zũciyar (Annabi) bata ƙaryata abin da ya gani ba.
Verse 12
ﮈﮉﮊﮋ
ﮌ
Shin, zã ku yi masa musu a kan abin da yake gani?
Verse 13
ﮍﮎﮏﮐ
ﮑ
Kuma lalle ya gan shi, haƙĩƙatan, a wani lõkacin saukarsa.
Verse 14
ﮒﮓﮔ
ﮕ
A wurin da magaryar tuƙẽwa take.
Verse 15
ﮖﮗﮘ
ﮙ
A inda taken, nan Aljannar makoma take.
Verse 16
ﮚﮛﮜﮝﮞ
ﮟ
Lõkacin da abin da yake rufe magaryar tuƙẽwa ya rufe ta.
Verse 17
ﮠﮡﮢﮣﮤ
ﮥ
Ganinsa bai karkata ba, kuma bai ƙetare haddi ba.
Verse 18
ﮦﮧﮨﮩﮪﮫ
ﮬ
Lalle, tabbas, (Annabinku) ya ga waɗanda suka fi girma daga ãyõyin Ubangijinsa.
Verse 19
ﮭﮮﮯ
ﮰ
Shin, kun ga Lãta da uzza?
Verse 20
ﮱﯓﯔ
ﯕ
Da (wani gunki wai shi) Manãta, na ukunsu?
Verse 21
ﯖﯗﯘﯙ
ﯚ
Ashe, kũ ne da ɗa namiji Shĩ (Allah) kuma da ɗiya mace?
Verse 22
ﯛﯜﯝﯞ
ﯟ
Wannan fa ya zama rabo naƙasasshe.
Verse 23
Waɗannan bã kõme ba ne fãce sũnãye, waɗanda kuka ambace su da su, kũ da uwãyenku. Allah bai saukar da wani dalĩli game da su ba. (Kãfirai) bã su biyar kõme fãce zato da abin da rãyukansu ke so, Alhãli kuwa shiriyar ta daga wajen Ubangijinsu, ta jẽ musu (sai suka bar ta suka kõma wa zaton).
Verse 24
ﯼﯽﯾﯿ
ﰀ
Ko (an fai cẽwa) mutum zai sãmi abin da yake gũri?
Verse 25
ﰁﰂﰃ
ﰄ
To, Lãhira da dũniya na Allah kawai ne (wanda ya nẽme su daga wani, yã yi kuskure).
Verse 26
Akwai malã'iku da yawa a cikin sammai cẽtonsu bã ya wadãtar da kõme fãce bãyan Allah Yã yi izni (da shi) ga wanda Yake so, kuma Yake yarda.
Verse 27
Lalle waɗannan da bã su yin ĩmãni da Lãhira, haƙĩƙa sunã kiran malã'iku da sũnan mace.
Verse 28
Kuma bã su da wani ilmi game da shi, bã su bin kõme fãce zato alhãli kuwa lalle zato bã ya amfãnar da kõme daga gaskiya.
Verse 29
Sabõda haka sai ka kau da kai daga wanda ya jũya bãya daga ambatonMu kuma bai yi nufin kõme ba fãce rãyuwar kusa (dũniya).
Verse 30
Wannan ita ce iyãkar abin da suke iya kai gare shi na ilmi. lalle Ubangijinka Shĩ ne Mafi sanin wanda ya ɓace daga hanyarSa, kuma Shi ne Mafi sani ga wanda ya nẽmi shiriya.
Verse 31
Kuma abin da ke cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasã na Allah kawai ne, dõmin Yã sãka wa waɗanda suka mũnana da abin da suka aikata, kuma Ya sãka wa waɗanda suki kyautata da sakamakon da ya fi kyau.
Verse 32
Waɗanda ke nĩsantar manyan zunubai da abũbuwan alfãsha, fãce ƙanãnan laifuffuka, lalle Ubangijinka Mai yalwatattar gãfara ne, Shĩ ne Ya fi sani ga abinda ke gare ku a lõkacin da Ya ƙãga halittarku daga ƙasa, kuma a lõkacin da kuke tãyuna a cikin cikannan uwãyenku. Sabõda haka, kada ku tsarkake kanku, Shĩ ne Mafi sani ga wanda ya yi taƙawa.
Verse 33
ﯢﯣﯤ
ﯥ
Shin, ka ga wannan da ya jũya baya?
Verse 34
ﯦﯧﯨ
ﯩ
Ya yi kyauta kaɗan, kuma ya yi rowa?
Verse 35
ﯪﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
Shin, akwai ilmin gaibi a wurinsa, Sabõda haka yanã ganin gaibin?
Verse 36
Ko kuwa ba a ba shi lãbãri ba ga abin da yake a cikin Littafan Mũsã?
Verse 37
ﯸﯹﯺ
ﯻ
Da Ibrãhĩm wanda ya cika alkawari?
Verse 38
ﯼﯽﯾﯿﰀ
ﰁ
Cẽwa wani rai mai kãyan laifi bã ya ɗaukar kãyan laifin wani.
Verse 39
ﰂﰃﰄﰅﰆﰇ
ﰈ
Kuma mutum bã shi da kõme fãce abin da ya aikata.
Verse 40
ﰉﰊﰋﰌ
ﰍ
Kuma lalle, aikinsa zã a gan shi.
Verse 41
ﰎﰏﰐﰑ
ﰒ
Sa'an nan a sãka masa da sakamako wanda yake mafi cikar ma'auni?
Verse 42
ﰓﰔﰕﰖ
ﰗ
Kuma lalle, makõmar zuwa Ubangijinka kawai take?
Verse 43
ﰘﰙﰚﰛ
ﰜ
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya sanya dariya, kuma Ya sanya kũka.
Verse 44
ﰝﰞﰟﰠ
ﰡ
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya kashe, kuma Ya rãyar.
Verse 45
ﭑﭒﭓﭔﭕ
ﭖ
Kuma lalle Shĩ ne Ya yi halitta nau'i-nau'i, namiji da mace.
Verse 46
ﭗﭘﭙﭚ
ﭛ
Daga wani ɗigon ruwa guda a lõkacin da ake jẽfa shi a cikin mahaifa.
Verse 47
ﭜﭝﭞﭟ
ﭠ
Kuma a kansa ne ƙãga halitta ta biyu take.
Verse 48
ﭡﭢﭣﭤ
ﭥ
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya azurta, kuma Ya wadãtar.
Verse 49
ﭦﭧﭨﭩ
ﭪ
Kuma lalle, Shĩ, Shi ne Ubangijin Shi'ira.
Verse 50
ﭫﭬﭭﭮ
ﭯ
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya halaka Ãdãwa na farko.
Verse 51
ﭰﭱﭲ
ﭳ
Da Samũdãwa, sa'an nan bai rage su ba.
Verse 52
Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sũ sun kasance mafi zãlunci kuma mafi girman kai.
Verse 53
ﭿﮀ
ﮁ
Da waɗanda aka birkice ƙasarsu, Ya kãyar da su.
Verse 54
ﮂﮃﮄ
ﮅ
Sa'an nan abin da ya rufe su, ya rufe su.
Verse 55
ﮆﮇﮈﮉ
ﮊ
To, da wace daga ni'imõmin Ubangijinka kake yin shakka?
Verse 56
ﮋﮌﮍﮎﮏ
ﮐ
wannan (Muhammadu) mai gargaɗi ne kamar irin mãsu gargaɗi na farko.
Verse 57
ﮑﮒ
ﮓ
Makusanciya fa, tã yi kusa.
Verse 58
ﮔﮕﮖﮗﮘﮙ
ﮚ
Bãbu wani rai, banda Allah, mai iya bãyani gare ta.
Verse 59
ﮛﮜﮝﮞ
ﮟ
Shin, kuma daga wannan lãbãri kuke mãmãki?
Verse 60
ﮠﮡﮢ
ﮣ
Kuma kunã yin dãriya, kuma bã ku yin kũka?
Verse 61
ﮤﮥ
ﮦ
Alhãli kunã mãsu wãsã?
Verse 62
ﮧﮨﮩﮪ
ﮫ
To, ku yi tawãli'u ga Allah, kuma ku bauta (masa).
تقدم القراءة