Fassarar Surar Al-Inshikak a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
Verse 1
ﭣﭤﭥ
ﭦ
Al-Inshikak
Idan sama ta kẽce,
Verse 2
ﭧﭨﭩ
ﭪ
Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,
Verse 3
ﭫﭬﭭ
ﭮ
Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,
Verse 4
ﭯﭰﭱﭲ
ﭳ
Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.
Verse 5
ﭴﭵﭶ
ﭷ
Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,
Verse 6
Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.
Verse 7
ﮁﮂﮃﮄﮅ
ﮆ
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.
Verse 8
ﮇﮈﮉﮊ
ﮋ
To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.
Verse 9
ﮌﮍﮎﮏ
ﮐ
Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.
Verse 10
ﮑﮒﮓﮔﮕﮖ
ﮗ
Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.
Verse 11
ﮘﮙﮚ
ﮛ
To, zã shi dinga kiran halaka!
Verse 12
ﮜﮝ
ﮞ
Kuma ya shiga sa'ĩr.
Verse 13
ﮟﮠﮡﮢﮣ
ﮤ
Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.
Verse 14
ﮥﮦﮧﮨﮩ
ﮪ
Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.
Verse 15
Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.
Verse 16
ﯔﯕﯖ
ﯗ
To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.
Verse 17
ﯘﯙﯚ
ﯛ
Da dare, da abin da ya ƙunsa.
Verse 18
ﯜﯝﯞ
ﯟ
Da watã idan (haskensa) ya cika.
Verse 19
ﯠﯡﯢﯣ
ﯤ
Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.
Verse 20
ﯥﯦﯧﯨ
ﯩ
To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?
Verse 21
Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u?
Verse 22
ﯲﯳﯴﯵ
ﯶ
Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.
Verse 23
ﯷﯸﯹﯺ
ﯻ
Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.
Verse 24
ﯼﯽﯾ
ﯿ
Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.
Verse 25
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa.
تقدم القراءة