Fassarar Surar A-Hijr a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
Verse 1
A-Hijr
A. L̃.R. Waɗancan ãyoyin littãfi ne da abin karantãwa mai bayyanãwa.
Verse 2
Da yawa waɗanda suka kãfirta suke gũrin dã dai sun kasance Musulmi.
Verse 3
Ka bar su su ci kuma su ji dãdi, kuma gũri ya shagaltar da su, sa'an nan da sannu zã su sani.
Verse 4
Kuma ba Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da littafi sananne.
Verse 5
Wata al'umma bã ta gabãtar ajalinta, kuma bã zã su jinkirta ba.
Verse 6
Suka ce: "Yã kai wanda aka saukar da Ambato (Alƙur'ãni) a kansa! Lalle ne kai, haƙĩƙa, mahaukaci ne."
Verse 7
"Dõmin me bã zã ka zo mana da malã'ĩku ba idan ka kasance daga mãsu gaskiya?"
Verse 8
Bã Mu sassaukar da malã'iku fãce da gaskiya, bã zã su kasance, a wannan lõkacin, waɗanda ake yi wa jinkĩri ba.
Verse 9
Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur'ãni), kuma lal1e Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayẽwane gare shi.
Verse 10
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika Manzanni a cikin ƙungiyõyin farko, gabãninka.
Verse 11
Kuma wani Manzo bã ya zuwa gare su fãce sun kasance sunã mãsu, izgili a gare shi.
Verse 12
ﮰﮱﯓﯔﯕ
ﯖ
Kamar wancan ne Muke shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.
Verse 13
Bã su yin ĩmãni da shi, kuma haƙĩƙa, hanyar mutãnen farko ta shige.
Verse 14
Kuma dã Mun bũɗe wata ƙõfa daga sama a kansu har suka wuni a ciki sunã tãkãwa.
Verse 15
Lalle ne dã sun ce: "Abin sani kawai, an rufe idãnuwanmu ne. Ã'a, mũ mutãne ne waɗanda aka sihirce."
Verse 16
Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun sanya waɗansu masaukai a, cikin sama, kuma Muka ƙawãta ta ga masu kallo.
Verse 17
ﭙﭚﭛﭜﭝ
ﭞ
Kuma Muka kiyãye ta daga dukan Shaiɗani wanda ake jĩfa.
Verse 18
Fãce wanda ya sãci saurãre sai wutar yũlã bayyananniya ta bĩ shi.
Verse 19
Kuma ƙasa Mun mĩkẽ ta kuma Mun jẽfa duwãtsu tabbatattu a cikinta kuma Mun tsirar a cikinta, daga dukan abu wanda ake aunãwa da sikẽli.
Verse 20
Kuma Muka sanyã muku, a cikinta, abũbuwan rãyuwã da wanda ba ku zamã mãsu ciyarwa gare shi ba.
Verse 21
Kuma bãbu wani abu fãce a wurinMu, akwai taskõkĩnsa kuma ba Mu saukar da shi ba fãce kan gwargwado sananne.
Verse 22
Kuma Muka aika iskõki mãsu barbarar jũna sa'an nan Muka saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Muka shãyar da ku shi, kuma ba ku zama mãsu taskacẽwa a gare shi ba.
Verse 23
ﮕﮖﮗﮘﮙﮚ
ﮛ
Kuma lalle ne Mu Muke rãyarwa, kuma Muke kashẽwa kuma Mũ ne magada.
Verse 24
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun san mãsu gabãta daga cikinku, kuma Mun san mãsu jinkiri.
Verse 25
Kuma lalle ne Ubangijinka Shĩ ne Yake tãra su, lalle Shĩ ne Mai hikima, Masani.
Verse 26
Kuma lalle ne Mun halicci mutum daga ƙeƙasasshiyar lãka, daga baƙin yumɓu wanda ya canja.
Verse 27
Kuma Aljani Mun haliccẽ shi daga gabãni, daga wutar iskar zafi.
Verse 28
Kuma a lõkacin da Ubangijinka ya ce wa malã'iku: "Lalle Nĩ mai halittar wani jiki ne daga ƙẽƙasasshen yumɓu wanda ya canja."
Verse 29
"To idan Na daidaitã shi kuma Na hũra daga RũhĩNa a cikinsa, to, ku fãɗi a gare shi, kunã mãsu yin sujada."
Verse 30
ﯶﯷﯸﯹ
ﯺ
Sai malã'iku suka yi sujada dukkansu gaba ɗaya.
Verse 31
Fãce Iblĩs, ya ƙi kasancẽwa daga mãsu yin sujadar.
Verse 32
Ya ce: "Yã Iblĩs mẽne ne a gare ka, ba ka kasance tãre da mãsu yin sujuda ba?"
Verse 33
Ya ce: "Ban kasance inã yin sujada ba ga mutum wanda Ka halicce shi daga bũsasshen yumɓun lãka wadda ta canja."
Verse 34
ﭦﭧﭨﭩﭪ
ﭫ
Ya ce: "To, ka fita daga gare ta, dõmin lalle kai abin jĩfa ne."
Verse 35
ﭬﭭﭮﭯﭰﭱ
ﭲ
"Kuma lalle ne akwai la'ana a kanka har ya zuwa rãnar sakamako."
Verse 36
ﭳﭴﭵﭶﭷﭸ
ﭹ
Ya ce: "Yã Ubangjĩna! Sai Ka yi mini jinkiri zuwa rãnar da ake tãshin su."
Verse 37
ﭺﭻﭼﭽ
ﭾ
Ya ce: "To, lalle ne kanã daga waɗanda ake yi wa jinkiri."
Verse 38
ﭿﮀﮁﮂ
ﮃ
"Zuwa ga Yinin Lõkacin nan sananne."
Verse 39
Ya ce: "Yã Ubangijina! Inã rantsuwa da abin da Ka ɓatar da ni da shi, haƙĩƙa inã ƙawãta musu (rãyuwa) a cikin ƙasã kuma haƙĩƙa inã ɓatar da su gabã ɗaya."
Verse 40
ﮏﮐﮑﮒ
ﮓ
"Fãce bãyinKa daga gare su, waɗanda Ka tsarkake."
Verse 41
ﮔﮕﮖﮗﮘ
ﮙ
Ya ce: "Wannan tafarki ne a gare Ni, madaidaici."
Verse 42
"Lalle ne bãyĩNa, bã ka da ĩkõ a kansu, fãce wanda ya bĩ ka daga ɓatattu."
Verse 43
ﮦﮧﮨﮩ
ﮪ
Kuma lalle Jahannama ce haƙĩƙa, ma'a1kawartarsu gabã ɗaya.
Verse 44
Tanã da ƙõfõfi bakwai, ga kõwace ƙõfa akwai wani juz'i daga gare su rababbe.
Verse 45
ﯕﯖﯗﯘﯙ
ﯚ
Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna mai idandunan ruwa.
Verse 46
ﯛﯜﯝ
ﯞ
"Ku shigẽ ta da aminci, kunã amintattu."
Verse 47
Kuma Muka ɗẽbe abinda ke a cikin zukãtansu na daga ƙullin zũci, suka zama 'yan'uwa a kan gadãje, sunã mãsu fuskantar junã.
Verse 48
Wata wahala bã zã ta shãfe su bã a cikinta kuma ba su zama mãsu fita daga, cikinta ba.
Verse 49
Ka bai wa bãyiNa lãbari cẽwa lalle ne Ni, Mai gãfarane, Mai jin ƙai.
Verse 50
ﯻﯼﯽﯾﯿ
ﰀ
Kuma azãbãTa ita ce azãba mai raɗaɗi.
Verse 51
ﰁﰂﰃﰄ
ﰅ
Kuma ka bã su lãbãrin bãƙin Ibrãhĩm.
Verse 52
A lõkacin da suka shiga gunsa, sai suka ce: "Sallama." Ya ce: "Lalle mũ, daga gare ku, mãsu firgita ne."
Verse 53
Suka ce: "Kada ka firgita. Lalle ne mũ, munã yi makabushãra game da wani yãro masani."
Verse 54
Ya ce: "Shin kun bã ni bushãra ne a kan tsũfa yã shãfe ni? To, da me kuke bã ni bushara?"
Verse 55
Suka ce: "Munã yi maka bushãra da gaskiya ne, sabõda haka, kada da kasance daga mãsu yanke tsammãni."
Verse 56
Ya ce: "Kuma wãne ne yake yanke tsammãni daga rahamar Ubangijinsa, fãce ɓatattu?"
Verse 57
ﭽﭾﭿﮀﮁ
ﮂ
Ya ce: "To, mẽne ne babban al'amarinku? Yã kũ manzanni!"
Verse 58
ﮃﮄﮅﮆﮇﮈ
ﮉ
Suka ce: "Lalle ne mũ, an aika mu zuwa ga wasu mutãne mãsu laifi."
Verse 59
ﮊﮋﮌﮍﮎﮏ
ﮐ
"Fãce mutãnen Lũɗu, lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu tsĩrar dasu ne gabã ɗaya."
Verse 60
ﮑﮒﮓﮔﮕﮖ
ﮗ
"Fãce mãtarsa mun ƙaddara cẽwa lalle ne ita, haƙĩƙa, tanã daga mãsu halaka."
Verse 61
ﮘﮙﮚﮛﮜ
ﮝ
To, a lõkacin da mazannin suka jẽ wa mutãnen Lũɗu,
Verse 62
ﮞﮟﮠﮡ
ﮢ
Ya ce: "Lalle ne ku mutãne ne waɗanda ba a sani ba."
Verse 63
Suka ce: "Ã'a, mun zo maka sabõda abin da suka kasance sunã shakka a cikinsa."
Verse 64
ﮫﮬﮭﮮ
ﮯ
"Kuma mun zo maka da gaskiya. Kuma lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu gaskiya ne."
Verse 65
"Sai ka yi tafiya da iyãlinka, a wani yanki na dare, kuma ka bi bãyansu, kuma kada wani daga cikinku ya yi waiwaye, kuma ku bi ta inda aka aumurce ku."
Verse 66
Kuma Muka hukunta wancan al'amarin zuwa gare shi cẽwa lalle ne ƙarshen waɗancan abin yankẽwa ne a lõkacin da suke mãsu shiga asuba.
Verse 67
ﯪﯫﯬﯭ
ﯮ
Kuma mutãnen alƙaryar suka je sunã mãsu bushãra.
Verse 68
ﯯﯰﯱﯲﯳﯴ
ﯵ
Ya ce: "Lalle ne waɗannan bãƙĩna ne, sabõda haka kada ku kunyata ni."
Verse 69
ﯶﯷﯸﯹ
ﯺ
"Kuma ku bi Allah da taƙawa, kuma kada ku sanya ni a baƙin ciki."
Verse 70
ﯻﯼﯽﯾﯿ
ﰀ
Suka ce: "Ashe ba mu hana ka daga tãlikai ba?"
Verse 71
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
Ya ce: "Ga waɗannan, 'ya'yãna idan kun kasance mãsu aikatãwa ne."
Verse 72
ﭘﭙﭚﭛﭜ
ﭝ
Rantsuwa da rãyuwarka! Lalle ne sũ a cikin mãyensu sunã ta ɗĩmuwa.
Verse 73
ﭞﭟﭠ
ﭡ
Sa'an nan tsãwa ta kãma su, sunã mãsu shiga lõkacin hũdõwar rãnã.
Verse 74
Sa'an nan Muka sanya samanta ya kõma ƙasanta, kuma Muka yi ruwan duwãtsu na lãkar wuta a kansu.
Verse 75
ﭫﭬﭭﭮﭯ
ﭰ
Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi ga mãsu tsõkaci da hankali.
Verse 76
ﭱﭲﭳ
ﭴ
Kuma lalle ne ita, haƙĩƙa sunã a gẽfen wata hanyã tabbatacciya.
Verse 77
ﭵﭶﭷﭸﭹ
ﭺ
Lalle ne a cikin wancan akwai ãyã ga mãsu ĩmãni.
Verse 78
ﭻﭼﭽﭾﭿ
ﮀ
Kuma lalle ne ma'abũta Al'aika sun kasance, haƙĩƙa, mãsu zãlunci!
Verse 79
ﮁﮂﮃﮄﮅ
ﮆ
Sai Muka yi azãbar rãmuwã a gare su, kuma lalle sũ biyun, haƙĩƙa, sunã a gẽfen wani tafarki mabayyani.
Verse 80
ﮇﮈﮉﮊﮋ
ﮌ
Kuma lalle ne haƙĩƙa ma'abũta Hijiri sun ƙaryata Manzanni.
Verse 81
ﮍﮎﮏﮐﮑ
ﮒ
Kuma Kuka kai musu ãyõyinMu, sai suka kasance mãsu bijirẽwa daga gare su.
Verse 82
ﮓﮔﮕﮖﮗﮘ
ﮙ
Kuma sun kasance sunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, alhãli sunã amintattu.
Verse 83
ﮚﮛﮜ
ﮝ
Sai tsãwa ta kãma su sunã mãsu shiga asuba.
Verse 84
ﮞﮟﮠﮡﮢﮣ
ﮤ
Sa'an nan abin da suka kasance sunã tsirfantãwa bai wadãtar ga barinsu ba.
Verse 85
Kuma ba Mu halicci sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu ba fãce da gaskiya. Kuma lalle ne Sã'a (Rãnar Alƙiyãma) haƙĩƙa mai zuwa ce. Sabõdahaka ka yi rangwame, rangwame mai kyau.
Verse 86
ﯗﯘﯙﯚﯛ
ﯜ
Lalle ne Ubangijinka, shi ne Mai yawan halitta, Masani.
Verse 87
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bã ka bakwai waɗanda ake maimaita karatunsu da Alƙur'ãni mai girma.
Verse 88
Kada lalle kaƙĩƙa idãnunka biyu zuwa ga abin da Muka jiyar da su dãɗi game da shi, nau'i-nau'i a gare su, kuma kada ka yi baƙin ciki a kansu, kuma sassauta fikãfikanka ga mãsu ĩmãni.
Verse 89
ﯵﯶﯷﯸﯹ
ﯺ
Kuma ka ce: "Lalle nĩ nĩ ne mai gargaɗi bayyananne."
Verse 90
ﯻﯼﯽﯾ
ﯿ
Kamar yadda Muka saukar a kan mãsu yin rantsuwa,
Verse 91
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
Waɗanda suka sanya Alƙur'ãni tãtsuniyõyi.
Verse 92
ﭖﭗﭘ
ﭙ
To, rantsuwa da Ubangijinka! Haƙĩƙa, Munã tambayarsugabã ɗaya.
Verse 93
ﭚﭛﭜ
ﭝ
Daga abin da suka kasance sunã aikatãwa.
Verse 94
ﭞﭟﭠﭡﭢﭣ
ﭤ
Sai ka tsage gaskiya game da abin da ake umurnin ka kuma ka kau da kai daga masu shirki.
Verse 95
ﭥﭦﭧ
ﭨ
Lalle ne Mũ Mun isar maka daga mãsu izgili.
Verse 96
Waɗanda suke sanyãwar wani abin bautãwa na dabam tare da Allah, sa'an nan da sannu zã su sani.
Verse 97
Kuma lalle ne haƙĩƙa Munã sanin cẽwa lalle kai, ƙirjinka yanã yin ƙunci game da abin da suke faɗã (na izgili).
Verse 98
ﭻﭼﭽﭾﭿﮀ
ﮁ
Sabõda haka ka yi tasbĩhi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka kasance daga mãsu sujada.
Verse 99
ﮂﮃﮄﮅﮆ
ﮇ
Kuma ka bauta wa Ubangijinka, har mutuwa ta zo maka.
تقدم القراءة