Fassarar Surar As-Shams a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
Verse 1
ﭜﭝ
ﭞ
As-Shams
Ina rantsuwa da rãnã da hantsinta.
Verse 2
ﭟﭠﭡ
ﭢ
Kuma da wata idan ya bi ta.
Verse 3
ﭣﭤﭥ
ﭦ
Da yini a lõkacin da ya bayyana ta.
Verse 4
ﭧﭨﭩ
ﭪ
Da dare a lõkacin da ya ke rufe ta.
Verse 5
ﭫﭬﭭ
ﭮ
Da sama da abin da ya gina ta.
Verse 6
ﭯﭰﭱ
ﭲ
Da ƙasã da abin da ya shimfiɗa ta.
Verse 7
ﭳﭴﭵ
ﭶ
Da rai da abin da ya daidaita shi.
Verse 8
ﭷﭸﭹ
ﭺ
Sa'an nan ya sanar da shi fãjircinsa da shiryuwarsa.
Verse 9
ﭻﭼﭽﭾ
ﭿ
Lalle ne wanda ya tsarkake shi (rai) ya sãmi babban rabo.
Verse 10
ﮀﮁﮂﮃ
ﮄ
Kuma lalle ne wanda ya turbuɗe shi (da laifi) ya tãɓe.
Verse 11
ﮅﮆﮇ
ﮈ
Samũdãwa sun ƙaryata (Annabinsu), dõmin girman kansu.
Verse 12
ﮉﮊﮋ
ﮌ
A lõkacin da mafi shaƙãwarsu ya tafi (wurin sõke rãkumar sãlihu).
Verse 13
Sai Manzon Allah ya gaya musu cewa: "Ina tsõratar da ku ga rãƙumar Allah da ruwan shanta!"
Verse 14
Sai suka ƙaryata shi, sa'an nan suka sõke ta. Sabõda haka Ubangijinsu Ya darkãke su, sabõda zunubinsu. Sa'an nan Ya daidaita ta (azãbar ga mai laifi da maras laifi).
Verse 15
ﮝﮞﮟ
ﮠ
Kuma bã ya tsõron ãƙibarta (ita halakãwar).
تقدم القراءة