Fassarar Surar Al-Hakkah a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
Verse 1
ﮯ
ﮰ
Al-Hakkah
Kiran gaskiya!
Verse 2
ﮱﯓ
ﯔ
Mẽne ne kiran gaskiya?
Verse 3
ﯕﯖﯗﯘ
ﯙ
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?
Verse 4
ﯚﯛﯜﯝ
ﯞ
Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!
Verse 5
ﯟﯠﯡﯢ
ﯣ
To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.
Verse 6
ﯤﯥﯦﯧﯨﯩ
ﯪ
Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.
Verse 7
(Allah) Ya hõre ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da jũna, sabõda haka, kana ganin mutãne a cikinta kwance. Kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne, waɗanda suka fãɗi.
Verse 8
ﯼﯽﯾﯿﰀ
ﰁ
To, kõ kanã ganin abin da ya yi saurã daga cikinsu?
Verse 9
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.
Verse 10
ﭘﭙﭚﭛﭜﭝ
ﭞ
Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).
Verse 11
Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.
Verse 12
ﭧﭨﭩﭪﭫﭬ
ﭭ
Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).
Verse 13
ﭮﭯﭰﭱﭲﭳ
ﭴ
To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗaya.
Verse 14
ﭵﭶﭷﭸﭹﭺ
ﭻ
Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma aka niƙa su niƙãwa ɗaya.
Verse 15
ﭼﭽﭾ
ﭿ
A ran nan, mai aukuwa zã ta auku.
Verse 16
ﮀﮁﮂﮃﮄ
ﮅ
Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai rauni ce.
Verse 17
Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.
Verse 18
ﮑﮒﮓﮔﮕﮖ
ﮗ
A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.
Verse 19
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."
Verse 20
ﮢﮣﮤﮥﮦ
ﮧ
"Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."
Verse 21
ﮨﮩﮪﮫ
ﮬ
Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.
Verse 22
ﮭﮮﮯ
ﮰ
A cikin Aljanna maɗaukakiya.
Verse 23
ﮱﯓ
ﯔ
Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),
Verse 24
(Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."
Verse 25
Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!"
Verse 26
ﯩﯪﯫﯬ
ﯭ
"Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"
Verse 27
ﯮﯯﯰ
ﯱ
"In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!
Verse 28
ﯲﯳﯴﯵﯶ
ﯷ
"Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!"
Verse 29
ﯸﯹﯺ
ﯻ
"Ĩkona ya ɓace mini!"
Verse 30
ﯼﯽ
ﯾ
(Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."
Verse 31
ﯿﰀﰁ
ﰂ
"Sa'an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."
Verse 32
"Sa'an nan, acikin sarƙa, tsawonta zirã'i saba'in, sai ku sanya shi."
Verse 33
ﰋﰌﰍﰎﰏﰐ
ﰑ
"Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin ĩmãni da Allah, Mai girma!"
Verse 34
ﰒﰓﰔﰕﰖ
ﰗ
"Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci!"
Verse 35
ﰘﰙﰚﰛﰜ
ﰝ
"Sabõda haka, a yau, a nan, bã ya da masõyi."
Verse 36
ﭑﭒﭓﭔﭕ
ﭖ
"Kuma bãbu wani abinci, sai daga (itãcen) gislĩn."
Verse 37
ﭗﭘﭙﭚ
ﭛ
"Bãbu mai cin sa sai mãsu ganganci."
Verse 38
ﭜﭝﭞﭟ
ﭠ
To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,
Verse 39
ﭡﭢﭣ
ﭤ
Da abin da bã ku iya gani.
Verse 40
ﭥﭦﭧﭨ
ﭩ
Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.
Verse 41
Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku gaskata.
Verse 42
Kuma bã maganar bõka ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa.
Verse 43
ﭻﭼﭽﭾ
ﭿ
Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.
Verse 44
ﮀﮁﮂﮃﮄ
ﮅ
Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.
Verse 45
ﮆﮇﮈ
ﮉ
Dã Mun kãma shi da dãma.
Verse 46
ﮊﮋﮌﮍ
ﮎ
sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.
Verse 47
ﮏﮐﮑﮒﮓﮔ
ﮕ
Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbarMu) daga gare shi.
Verse 48
ﮖﮗﮘ
ﮙ
Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.
Verse 49
ﮚﮛﮜﮝﮞ
ﮟ
Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.
Verse 50
ﮠﮡﮢﮣ
ﮤ
Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.
Verse 51
ﮥﮦﮧ
ﮨ
Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙshẽni.
Verse 52
ﮩﮪﮫﮬ
ﮭ
Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma.
تقدم القراءة