سورة الحاقة

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Fassarar Surar Al-Hakkah a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Verse 1

Al-Hakkah


Kiran gaskiya!
Verse 3

Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?
Verse 4

Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!
Verse 5

To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.

Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.

Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.

Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).

Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.

Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).

Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.

A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.
Verse 23

Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),

(Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."
Verse 27

"In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!
Verse 30

(Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."
Verse 40

Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.

Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.
Verse 48

Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.

Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.
Verse 50

Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.
تقدم القراءة